Aminiya:
2025-03-22@13:06:53 GMT

Ɗan Nijeriya ya lashe kyautar Kundin Bajinta na Duniya a fagen ɗaukar hoto

Published: 15th, February 2025 GMT

Wani ɗan Nijeriya ɗan asalin Jihar Yobe, Saidu Abdulrahman, ya lashe kambun lambar yabo ta Kundin Bajinta na Duniya a matsayin wanda ɗaukar hotuna kai tsaye cikin sa’a ɗaya.

Bayanai sun ce a cikin mintuna 60 Sa’idu Abdulrahman mai shekara 28, ya ɗauki hotuna 897 masu ɗaukar hankali a watan Satumba na bara, lamarin da ba shi damar doke wanda ya lashe kambun na bara da hotuna 500.

Makwabta sun kai karar ma’aurata saboda carar zakaransu Kasuwanci: Yadda matan Arewa ke samun arziki daga cikin gidajensu

Da wannan ƙwazo ne Kundin Bajinta na Duniya wata Guinness World Records (GWR) ya karrama matashin da lambar yabo.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, matashin ya bayyana cewa, “ina mai farin cikin sanar da cewa, an karrama ni a hukumance da matsayin mai riƙe da kambun tarihi na Guinness saboda na mafi ɗaukan hotunan da yawa waɗanda na ɗauka cikin sa’a ɗaya!

Saidu Abdulrahman riƙe da kambun lambar yabo ta Kundin Bajinta na Duniya

“Karɓar shaidar lashe lambar yabo ta kudin Guinness World Records, sakamako ne na jajircewa ta da kuma goyon baya mara iyaka daga dangina da abokaina, da jagororina, da masu yi min fatan alkhairi waɗanda suka kasance tare da ni.”

Ya ce “Nasarar kafa wannan tarihi na ɗaukar hotuna 897 a cikin minti 60 kacal, ba tawa ce ni kaɗai ba; ta duk ɗan Nijeriya ce da ya amince da ni, ya taimaka min, ya kuma jinjina min tun daga lokacin da na fara har gama.”

“Kafa wannan tarihi shaida ce ta cewa za mu iya yin bajinta a duniya.”

Haka ita ma cikin wani saƙo da Kundin Bajintar ya wallafa, ya ce “Abdulrahaman ya yi yunƙurin kafa tarihin ne domin wayar da kan jama’a game da ɗaukar hoto a Nijeriya.

TRT dai ya ruwaito cewa an ba shi lambar yabon ce a garin Potiskum da ke Jihar Yobe, kana taron ya samun halartar jami’an gwamnatin jihar da ɗalibai da kuma masoyansa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kundin Bajinta na Duniya Sa idu Abdulrahman Kundin Bajinta na Duniya lambar yabo

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar

Fadar Shugaban Kasar Nijeriya, ta yi watsi da rahoton baya-bayan nan da kwamitin hulda da kasashen wajen Amurka ya fitar, wanda ya kafa hujja da amincewar majalisar dokokin kasar, na zargin kakaba wa wasu kiristoci takunkumi a kasar.

Mai bai wa shugaban kasa shawara a kan harkokin siyasa, Daniel Bwala, ya bayyana rahoton a matsayin wanda ba shi da tushe da makama, yana mai jaddada cewa; tun bayan lokacin da Shugaba Tinubu ya dare kan kujerar mulki a ranar 29 ga Mayun 2023, al’amuran cin zarafi, musamman ta fuskar addini suka yi matukar ja da baya.

Bwala, ya yi wannan furuci ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, wato na D; yana mai jaddada cewa, gwamnatinsu mai ci yanzu; ta himmatu wajen kokarin daidaita addinai a matsayin abu guda.

“Gwamnatin Bola Tinubu, koda-yaushe na kokarin bai wa addinai muhimmanci na musamman. Tun daga ranar 29 ga Mayun 2023, daidai lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya hau kan karagar mulki, ba a taba samun wasu matsaloli na tsananta wa Kiristoci a ko’ina a fadin wannan kasa ba”, kamar yadda ya rubuta.

Ya jaddada cewa, Nijeriya ta kasance kasa mai dauke da addinai daban-daban, sannan a kowane lokaci gwamnati na kokarin samar da zaman lafiya a tsakanin wadannan addinai.

Martanin da Fadar Shugaban Kasar ta mayar, ya biyo bayan nuna damuwa a kan matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta dauka na amincewa da takunkumin da aka kakaba wa Nijeriya, bisa zargin kashe Kiristoci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • Cibiya Mai Fafutukar Kare Hakkokin Falasdinawa “Global 195” Ta Shelanta Farautar Sojojin HKI Da Su KaTafka Laifukan Yaki
  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Zama Ƴar Amshin Shata — Kwankwaso
  • Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje
  • Sin: Shingayen Kasuwanci Suna Illata Wadatar Tattalin Arzikin Duniya
  • Manufofin Kasar Sin Sun Zamo Jagora Ga Duniya A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama
  • Iran: Jagora ya yi kira da a karfafa dogaro da kai a cikin gida domin dakile tasirin takunkumai
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12]
  • Alakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Bisa Daidaito Tsakanin Sin Da Amurka Za Ta Amfanar Da Kamfanonin Duniya