Ya ce wajibi ne Sin da Amurka su kauracewa rikici, idan ba haka, duniya ce za ta wahala. Sannan ya yi kira da a karfafa tattaunawa da inganta fahimta da karfafa aminci.

Ya ce kamata ya yi kasashen biyu su hada hannu wajen shawo kan kalubalen duniya, domin hakki ne da ya rataya a kan Sin da Amurka. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa

An kammala zagayen farko na tattaunawa tsakanin Iran da Amurka a babban birnin Muscat a shiga tsakanin kasar Oman.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da Steve Witkoff, manzon musamman na shugaban Amurka kan harkokin yankin gabas ta tsakiya ne suka jagoranci shawarwarin yau Asabar.

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Iran ta fitar ta ce bangarorin sun yi musayar ra’ayi game da shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya, da kuma dage takunkumi.

Ya kara da cewa an gudanar da shawarwarin ne cikin yanayi mai ma’ana kuma bisa mutunta juna.

A karshen sama da sa’o’i biyu da rabi na tattaunawar, shugabannin tawagogin Iran da na Amurka sun yi jawabi na ‘yan mintoci kadan a yayin da suke barin wurin taron a gaban ministan harkokin wajen Omani,” in ji ma’aikatar.

Bangarorin kuma zasu sake tattaunawa nan da mako mai zuwa, saidai ba’a bayyana takaimaimai wajen da tattauanwar za ta wakana ba.

A gefen tattaunawar, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baghaei ya shaidawa kafar yada labarai ta IRIB a birnin Muscat cewa, Iran na da manufa guda daya tabbatar da muradun kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran, Iraki Sun Karfafa Dangantakar Makamashi
  • Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasar
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Yaya ‘Yan Siyasar Amurka Ke Kasafta Harajin Ramuwar Gayya?
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  • Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu