Mahamoud Ali Youssouf Ya Zama Sabon Shugaban Kwamitin Gudanarwar AU
Published: 15th, February 2025 GMT
An zabi dan takarar kasar Djibouti Mahamoud Ali Youssouf a matsayin sabon shugaban kwamitin gudanarwar kungiyar tarayyar Afrika ta AU.
An zabe shi ne a yayin zaman taron kungiyar a birnin Addis Ababa na kasar Habasha da yammacin yau Asabar.
Ya samu nasara ne a zagaye na 7 da kuri’u 33 daga cikin 49.
Dan shekaru 59 da haihuwa, wanda shi ne ministan harkokin wajen kasar Djibouti zai gaji Moussa Faki Mahamat na Chadi wanda wa’adinsa na biyu kan shugabancin kungiyar zai kare a ranar 15 ga watan Maris.
Manyan kalubalen dake gaban sabon shugaban kwamitin gudanarwa na kungiyar ta AU sun hada da rikicin gabashin Jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango da Sudan da kuma matakin da shugaban Amurka Donald Trump ya dauka na rage taimakon da Amurka ke bayarwa, lamarin da ya shafi nahiyar.
A daya bangaren kuma an zabi Selma Haddadi ‘yar kasar Aljeriya a matsayin mataimakiyar shugaban kwamitin na Tarayyar Afirka.
Ta yi nasara da kuri’u 33 a kan sauran ‘yan takara biyu na Morocco da Masar.
Kungiyar mai kasashe 55 dake wakiltar kusan mutum biliyan 1.5 an dade ana sukarta kan rashin tabaka komai kan matsalolin da suka shafi nahiyar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa
Ya soki masu ra’ayin cewa dimukradiyya wani sharadi ne na ci gaba, yana mai cewa “karya ne” shi akwai wata kasa da ta ci gaba a karkashin tsarin dimukradiyya?.
Burkina24 ta nakalto cewa “Babu wata kasa da za a iya bayyanawa da ta ci gaba a dimukradiyya.
Ya ci gaba da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sadarwa, bayyanawa, da kuma fahimtar da mutane mene ne juyin juya hali.
Traore ya yi fice wajen yanke shawarar ce bayan hayewarsa a matsayin shugaban kasar da ke yammacin Afirka.
Shugaban mai shekaru 37 da haihuwa wanda ya hau karagar mulki a watan Satumban 2022 ta hanyar juyin mulkin da ya hambarar da shugaban kasar na wucin gadi Paul-Henri Damiba kwanan nan ya yi watsi da tayin Saudiyya na gina masallatai 200 a kasarsa.
Ya bukaci kasar Musulunci da ta gwammace ta saka hannun jari a wasu muhimman ayyukan more rayuwa wadanda za su amfani al’ummarsa kai tsaye.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp