HausaTv:
2025-03-22@13:25:36 GMT

Iran Da Lebanon Sun Tattauna Kan Dangantakar Dake A Tsakaninsu

Published: 15th, February 2025 GMT

Kasashen Iran da kuma Lebanon sun tattauna kan dangantakar dake a tsakaninsu dama halin da ake ciki a yankin.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da yammacin yau Asabar, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da takwaransa na Lebanon din Youssef Raji sun jaddada muhimmancin mutunta juna da hadin gwiwa.

Iran da Lebanon suna da dangantaka mai karfi da ta dogara da muradu guda, tare da ci gaba da tattaunawa don karfafa hadin gwiwa a cikin kalubalen da ake fama da shi a yankin.

Araghchi ya taya Youssef Raji murnar nadin da aka yi masa a matsayin sabon ministan harkokin wajen Lebanon, tare da yi masa fatan samun nasara a sabuwar gwamnatin Lebanon.

Ya jaddada mahimmancin raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta bangarori daban-daban da suka hada da siyasa, tattalin arziki, kasuwanci, da al’adu.

Ministocin sun kuma tattauna kan bukatar tattaunawa don warware batutuwan da suka shafi jigilar fasinjoji tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Bayar Da Rijiyoyin Burtsasai 66 Ga Al’ummomin Zimbabwe Dake Fama Da Karancin Ruwa

Kasar Sin ta mika rijiyoyin burtsatsai 66 ga wasu yankunan lardin Mashonaland na gabashin Zimbabwe, wadanda za su samar da ruwa mai tsafta ga mutane kimanin 16,500.

Rijiyoyin wadanda kamfanin gine-gine na Geo-Engineering na kasar Sin ya gina, wani bangare ne na aikin hakar rijiyoyin burtsatsai 300 ga larduna 4 na kasar Zimbabwe.

Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Karfafa Cinikayya Da Ketare Tare Da Fadada Bude Kofa Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i

Yayin bikin mika rijiyoyin da aka yi jiya, ministan kula da kananan hukumomi da ayyukan more rayuwa na kasar Daniel Garwe, ya ce aikin alama ce ta hadin gwiwa da tausayi da goyon baya daga aminiyarsu a kowanne yanayi watau kasar Sin, wanda aka yi domin tabbatar da samar da ruwa mai tsafta ga kowa.

Shi kuwa jami’in kula da harkokin kasuwanci da tattalin arziki na ofishin jakadancin Sin a Zimbabwe Huang Minghai, cewa ya yi, aikin ya kara karfafa hadin gwiwar Sin da Zimbabawe da ya shafe gomman shekaru. Ya ce cikin shekaru 10 da suka gabata, kasar Sin ta gina rijiyoyin burtsatsai sama da 1,000 a fadin kasar ta Zimbabwe, wadanda mutane kusan 400,000 ke ci gajiyarsu. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Bayar Da Rijiyoyin Burtsasai 66 Ga Al’ummomin Zimbabwe Dake Fama Da Karancin Ruwa
  • An Yi Tarukan Tattaunawar Kasa Da Kasa Kan More Damammakin Sin A Havana Da Doha
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
  • Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Haren Kan Wasu Wurare A Gabaci Da Kuma Kudancin Kasar Lebanon
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Yaffa Kusa Da Tel Aviv A Karo Na Biyu A Cikin Sa’o’i 24
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu
  • An Gudanar Da Tarukan Tattaunawa Na Kasa Da Kasa Masu Jigon “Sin A Yanayin Bazara” A Turkiya Da Colombia
  • Iran : hare-haren Isra’ila a Gaza ci gaba da kisan kare dangi ne
  • Trump, ya ce ya yi tattauna mai armashi da Zelensky, bayan wacce ya yi da Putin