Iran Da Lebanon Sun Tattauna Kan Dangantakar Dake A Tsakaninsu
Published: 15th, February 2025 GMT
Kasashen Iran da kuma Lebanon sun tattauna kan dangantakar dake a tsakaninsu dama halin da ake ciki a yankin.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da yammacin yau Asabar, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da takwaransa na Lebanon din Youssef Raji sun jaddada muhimmancin mutunta juna da hadin gwiwa.
Iran da Lebanon suna da dangantaka mai karfi da ta dogara da muradu guda, tare da ci gaba da tattaunawa don karfafa hadin gwiwa a cikin kalubalen da ake fama da shi a yankin.
Araghchi ya taya Youssef Raji murnar nadin da aka yi masa a matsayin sabon ministan harkokin wajen Lebanon, tare da yi masa fatan samun nasara a sabuwar gwamnatin Lebanon.
Ya jaddada mahimmancin raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta bangarori daban-daban da suka hada da siyasa, tattalin arziki, kasuwanci, da al’adu.
Ministocin sun kuma tattauna kan bukatar tattaunawa don warware batutuwan da suka shafi jigilar fasinjoji tsakanin kasashen biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassa Al-Mujtaba (a) 107
107-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na Kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin al-kur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da Littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawi na maulana Jalaluddin Rumi, ko kuma cikin wasu littafan. Da fatana masu sauraro zasu kasance tare da mu.
///.. Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan lamami na biyu daga limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All…(s) kuma da na farko ga Fatimah (s) diyar manzon All..(s).
A cikin shirimmu da ya gabata mun bayyana yadda siyasar khalifa na uku na rabon kudade inda muka bayyana yadda ya kebe wasu daga cikin danginsa na kusa da shi da kudade masu yawa, wannan kuwa duk tare da korafe-korafen wasu daga cikin manya-manyan sahabban manzon All..(s).
Mun ji yadda ya ware kudade masu yawa ya bawa, danginsa banu Umayya wadanda suka hada da Abusufyan, Marwan dan hakan, Da Hakam din, da Abdullahi dan Abisarkh da da sauransu. Wadanda wasunsu sun cutar da manzon All..(s) saida ya la’anesu wasu ya koresu daga madina, wasu daga cikinsu ya bada umurnin a kashesu ko da an gansu rike da rigar dakin Kaaba.
Sannan ya nisanta dangin manzon All…(s) a cikin mafi yawan al-amuransa, sannan kamar yadda zamu gani, ya nisantar da wadanda suke tare da su. Ya kuma wulakantasu da sauransu.
Wani abin mamaki da khalifa Uthman yayi shi ne, ya dauki gonar Fadak, wacce ya ga yadda Zahra (d) diyar manzon All..(s) ta kai ruwa rana da Khalifa Abubakar ya mayar mata don hakkinta ne, wanda manzon All..(s) ya bata, kyauta gareta ga kuma yayanta a bayanta, ya bawa Marwan dan Hakan.
Idan kuda tare da mu a cikin shirye-shiryemmu na baya, mun bayyana cewa ayoyin alkur’ani ne suka sauka suka mallakawa manzon All..(s) gonar fadak sannan wasu ayoyin suka sauka suka mallakawa Zahrah(s) wannan gonar Amma Khalifa Abubakar ya kwace ta daga Zahrah (a) sannan daga karshe bayan shekaru kimani 16 gonar da Fadak ta zama mallakar dan wanda manzon All…(s) ya kora daga Madina.
Kamar yadda muka bayyana wannan halin da Khalifa Uthman ya kaiga, sahabban manzon All..(s) da dama sun koka a gabansa, sun bayyana masa cewa bai yi dai-dai.
Al-amarin ya kaiga, Andurrahman dan Auf, wanda ya zabe shi a matsayin Khalifa, bayan wafatin Khalifa na biyu, ya fahinci cewa yayi barna, ya je yana fadawa Aliyu dan Abitalib (a) kan cewa, ka dauka takobinka, ni ma zan dauki takobina, don ya sauya daga alkawalin da yayi mani. Sai Imam Ali (a) ya yi banza da shi. Sannan ya kai ga a lokacinda Abdurrahman dan Auf zai mutu ya bar wasiyya kada a bar Khalifa Uthman yayi masa sallah.
A lokacinda yake bada wannan kyauta da danginsa, yana cewa su dangi nane, sai suka ce masa, shin Abubakar da Umar basa da dangi ne?, sai ya amsa da cewa, Abubakar da Umar sune neman lada wajen All..saboda hana danginsu dukiyar jama’a dake hannunsu, amma ni kuma ina neman ladar amma da basu dukiyar.
A lokacinda sukar ta yi yawa, sai Khalifa Uthman ya nemi afwar mutane, kan dukiyar jama’a da ya bawa danginsa.
Amma yayi haka ba tareda ya dawo da dukiyoyin da ya basu ba, kuma bai san cewa ba’a kyauta sai da dukiyar da ya mallaka ba?.
Amirulmuminina (a) ya bada kekkyawar misala a lokacinda mutane suka dora masa khalifanci a bayan kissan Khalifa Uthman.
Inda yayansa Akili dan Abitalib ya zo wajensa a kufa, cikin talaucinsa, ya bukaci Amirul muminina (a) ya bashi dukiya daga baitul malin musulmi kamar yadda Khalifa Usman yake yi don ya biya basussukan da ake binsa.
Sai nawa ne basussukan da ake binka? Sai yace . Dinari dub 100.
Sai Imam (a) yace, bani da su, amma ka jira idan an yi albashi in baka wani abu daga cikinsa.
Sai Akil yace masa, baitul Mali yana hannunka amma kana cewa sai ka rabon albashinka ya fita? Sai Imam yace masa, kana umurtata in baka dukiyar musulmi, bayan sun sanyani amintaccensu a kanta?. Har zuwa karshen maganarsu.
Kunji yadda shugaban kuma khalifan musulmi yakamata ya kasance.
Banda haka hadisai da dama sun tabbata daga manzon All..(s) wadan nan wadanda Khalifa Uthman yake rabawa dukiyar musulmi, la’ananu ne a cikin alkur’ani mai girma.
An karbo Hadisi daga Hakika ibnu Abihatin ya rawaito daga Ibn Amru daga manzon All..(s) yana cewa : Na yi mafarkin yayan Hakam dan Abi Ass sun haw kan mimbarori kamar birrai, sai All..ya sauka da iyar da take cewa {Kuma bamu sanya mafarkin da muka nuna maka ba face fitinah, ga mutane, da kuma la’ananniyar itaciya}…yana nufin Hakam da yakan da yayansa,
Ummulmuminina A’isha ta fadawa Marwan dan Hakam kan cewa na ji manzon All..(s). yana fadawa babanka, (Abil Ass dan Umayya) Ku ne itaciyar da aka la’anta a cikin alkur’ani, kuma hakika ya hana son wadanda suke adawa da shi, ya haramta sadar da zumunci da su. All..T yana cewa: {Ba zakat aba samun mutanen wadanda suka yi Imani da All..da ranar lahira suna son wanda suke kiyayya da All..da manzonsa (s).ko da kuwa sun kasance iyayensu, ko yayansu, ko yan uwansu ko kuma danginsu ba}. Akwai hadisai da dama da suka yi magana a kan wanna sanna.
Sannan dangane da walid dan uqba wanda khalifa na uku ya sa a matsayin walin Kufa, a baya mun bayyana yadda ya sami sabani da Abdullahi dan Masa’ud wanda ya kasance mai kula da baulmalin musulmi a Kufa, amma daga baya khalifa ya fadawa masa cewa shi mai ajiya ne amma bai da iko ya fadi inda za’a kashe kudaden.
A nan ne ya bar aikin ya kuma koma madina.
To wannan Walid din da nassan Al-kur’ani shi fasiki, inda All..Ta yake cewa : {..idan fasiki ya zo maku da labari ku nemi bayani ..}. Mazon All..ya aike shi zuwa karban Zakka a wajen Banu Mustalak, ya karbi zakka, amma sai ya je ya zagaya ya dawo yace aiki sun ki su bayar, sai manzon All..(s) ya shirya yaki zuwa can, kafin ya isa wannan ayar ta sauka ta kira shi fasiki.
Banda haka walid mutum ne mai cike da kiyayyan ga musulunci saboda mahaifinsa Ukbatu dan Abi rabii, ya cutar da manzon All…(s) a makama, inda ya tofa yau a faskansa ya zageshi, sannan manzon All..(s) ya ce masa idan na sameka a wajen makka sai na kashe ka.
Sai gashi ya je yakin Badar aka kama shi a cikin fursinonin yaki, manzon All..(s) ya fidda shi daga sauran fursinoni ya kuma sa Aliyu ya sare wuyarsa ya kashe shi. Don haka wadannan al-amura suka hadu suka sanya walid mikiyin manzon All..(s) da Aliyu (a) da ma addinin musulunci, to yaya Khalifa Uthman zai bashi shigabanci a kan musulmi, a kuma manya manyan birane kamar Kufa?
Garin kufa babban gari ne wanda ya tattara baki daga cikin sabbin musulunta da bayi wadanda suke bukatar sahabbai koprarro a cikin sanin hukunce hukuncen addini don ko koya masu addinin, su nuna masu halaye masu kyua na addini, wadanda basu musulunta daga cikinsu su jawosu zuwa ga addinin musulunci, da halaye masu kyau ko hikimomi na addini. Irin wadanan musulmi idan sun ga abinda Walid yayi ko yake yi, ina zasu yi sha’awar shiga addinin musulunci.?
Maganar walida bata karewa, don bayan ya sha giya sannan ya bada sallar asubaha yana cikin maye, sannan yayi masu sallar asubaha raka’o’ii 4 sannan ya juya y ace masu in kara maku ne? banda haka ya yi aman giya a mihrabin sallah. Sai mutanen kufa suka ga cewa ba zasu iya ba.
Suka cire zubensa na zinari suka je madina suka kai kararsa wajen Khalifa. Khalifa Uthman bai ji dadi ba, sai suka garzaya zuwa wajen Imam Aliyu dan Abitalib (a), wanda ya shiga wajen Khalifa ya yi masa magana, a nan ne ba da sonsa ba, ya aikawa walid ya dawo Madina, da ya dawo, wadan mutane suka zo suka shaida kan cewa ya sha giya. Sannan walida ya kasa musanta hakan. Sai hadda ya tabbata a kansa. Amma aka rasa wa zai zo ya yi masa bulala 80 wanda shi ne haddin All..ga wanda ya sha giya aka kasa, samu saboda an san irin kusancinsa da Khalifa.
A nan ne sai Aliyu dan Abitalib (a) ya zo ya dauki bulala ya zaneshi, ya zartar masa da hadda, Khalifa yana turmude da fuskansa, har yana tsawo ga Aliyu kada ka masa haka, kada ka masa haka..!.
Ana gama wannan sai Khalifa ya tausaya masa, ya bashi aikin karbo zakka daga kabilar Kalb, ya je ya karbo zakka, ya dawo Khalifa ya bashi dukkan abinda ya karbo, kamar yadda muka yi bayani a baya.
Sannan abin mamaki sai Khalifa ya tura Sa’id dan Ass wanda shi ma matashi ne daga cikin matasan banu umayya. Sannan halayensa mai yuwa kadan ne ya fi Walid. Shima ya je yayi tasa barnan a kufa.
Kada ku manta Imam Hassan (a) wanda muke kawo maku sirarsa yana sane da wadannan abubuwa, kuma yana rike da su. Saboda su zama masa darasi kan yadda zai tafiyar da al-amura a lokacinda khalifanci zai shiga hannunsa.
Ya san yadda zai fuskance wadannan mutane, wadanda suka zama fitina babba a cikin musulmi kawo ke tsammani.
Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All…ya kaimu wassalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu.