Hamas Ta Saki ‘Yan Isra’ila Uku Kan Falasdinawa 369 A Musayar Fursunoni Ta Shida
Published: 15th, February 2025 GMT
kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta mika wasu ‘yan Isra’ila uku da ta yi garkuwa da su ga kungiyar agaji ta Red Cross a wani musayar fursunonin da aka sako Falasdinawa 369 a wata musanya ta baya-bayan nan a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta.
An saki ‘yan Isra’ilan uku a birnin Khan Yunus da ke kudancin Gaza, inda Isra’ilawan suka yi jawabi ga jama’a kafin mika su ga kungiyar agaji ta Red Cross.
Sakin dai shi ne na shida tun bayan da tsagaitawar ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu bayan fargabar da ake yi a makon da ya gabata cewa yarjejeniyar ta kusa rugujewa bayan da Isra’ila ta ki ba da isassun kayan agaji a Gaza.
Yawancinsu fursunoni falasdinawan da aka saki wadanda aka kama ne a zirin Gaza bayan harin ba zata da kungiyar ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba.
Yarjejenitar tsagaita bude wuta ta shiga cikin tsaka mai wuya tun bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya tayar da cece-kuce kan “kwace” Gaza, da tilastawa mutanen Zirin kaura zuwa Jordan da kuma Masar.
A karkashin Yarjejeniyar tsagaita bude wutar ana sa ran sakin ‘yan Isra’ila 33 yayin kan fursuninin falasdinawa 1,900.
Kawo yanzu an saki Isra’ilawa 16, kan fursunoni 765 na Falasdinawa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin HKI Sun Kara Kisan Karin Falasdinawa 71 A Zirin Gaza
Rahotannin da suke fitowa daga yankin Gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye sun nuna cewa, a cikin sa’o’ii 24 da suka gabata Falasdinawa 71 ne suka yi shahada a yayinda wasu da dama suka ji rauni.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a wannan karon jiragen yakin HKI da jiragen ruwan yake daga tekun medeteranina sun cilla wuta kan garuruwan Beit –Lahia, Rafah da kuamKhan Yunus inda suka kashe da dama ko suka kaisu ga shahada.
Labarin ya kara da cewa sojojin yahudawan sun sake mamayar yankin Netzarim wanda ya raba arewa da kudancin zirin gaza a yau Alhamis.
Ya zuwa yanzu yawan falasdinawa da suka yi shahada ya kai 49,547 tun fara yakin Tufanul Aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023, sannan yawan wadanda suka ji raunikuma ya karu zuwa 112,719 kamar yadda ma’aikatar lafiya ta zirin gaza ta bayyana.
HKI ta koma yaki bayan da ta yi watsi da tsagaita wuta da kungiyar Hamas, ita kadai a ranar Talanta da ta gabata.
A cikin kwanaki uku da suka gabata HKI ta kashe Falasdinawa kimani 500 a yankin Gaza. Inda kasha 2/3 daga cikinsu mata da yara ne.