HausaTv:
2025-02-20@08:59:09 GMT

Hamas Ta Saki ‘Yan Isra’ila Uku Kan Falasdinawa 369 A Musayar Fursunoni Ta Shida

Published: 15th, February 2025 GMT

kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta mika wasu ‘yan Isra’ila uku da ta yi garkuwa da su ga kungiyar agaji ta Red Cross a wani musayar fursunonin da aka sako Falasdinawa 369 a wata musanya ta baya-bayan nan a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

An saki ‘yan Isra’ilan uku a birnin Khan Yunus da ke kudancin Gaza, inda Isra’ilawan suka yi jawabi ga jama’a kafin mika su ga kungiyar agaji ta Red Cross.

Sakin dai shi ne na shida tun bayan da tsagaitawar ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu bayan fargabar da ake yi a makon da ya gabata cewa yarjejeniyar ta kusa rugujewa bayan da Isra’ila ta ki ba da isassun kayan agaji a Gaza.

Yawancinsu fursunoni falasdinawan da aka saki wadanda aka kama ne a zirin Gaza bayan harin ba zata da kungiyar ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba.

Yarjejenitar tsagaita bude wuta ta shiga cikin tsaka mai wuya tun bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya tayar da cece-kuce kan “kwace” Gaza, da tilastawa mutanen Zirin kaura zuwa Jordan da kuma Masar.

A karkashin Yarjejeniyar tsagaita bude wutar ana sa ran sakin ‘yan Isra’ila 33 yayin kan fursuninin falasdinawa 1,900.

Kawo yanzu an saki Isra’ilawa 16, kan fursunoni 765 na Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya

Jaridar Ma’ariv ta Isra’ila ta bayyana adadin wadanda suka jikkata a cikin sojojin mamayar Isra’ila da kuma miliyoyin yahudawan sahayoniyya da suka samu matsalar tabin hankali a lokacin yakin Gaza

Jaridar “Ma’ariv” ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta bayyana a jiya litinin, adadin wadanda suka mutu a cikin jerin sojojin mamayar Isra’ila a yayin mummunan ayyukan ta’addancin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar kan Zirin Gaza, wanda ya shafe tsawon watanni 15 kafin cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da musayar fursunoni a watan Janairun da ya gabata.

A cewar jaridar, sojoji 15,000 da ke cikin sojojin mamayar Isra’ila suka jikkata tun farkon yakin ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta 2023, yayin da wasu 846 suka sheka lahira.

Daga cikin wadanda suka samu raunuka, sojoji 8,600 ne suka sami raunuka daban-daban na jiki, yayin da wasu 7,500 suka samu matsalolin tabin kwakwalluwa ciki har da firgita, damuwa, tashin hankali, rikirkicewar tunani, kamar yadda jaridar ta nakalto daga sashin  kula da dabi’ar ma’aikata da ke karkashin Ma’aikatar yakin haramtacciyar kasar Isra’ila.

Kanun labarai

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Ce Tana Iya Sakin Dukkan Fursinonin Yahudawa Gaba Daya A Lokaci Guda
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Watsi Da Karin Shuruddan Gwamnatin ‘Yan Sayoniyya Kan Tsagaita Bude Wuta
  • Hamas: Za A Mika Gawawwakin ‘Yan Mamaya Da Kuma Fursunoni Rayayyu A Ranakun Alhamis Da Asabar
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Sun Baiwa Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Damar Ya Aikata Abin Da Yake So
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Hamas Ta Yabawa Tarayyar Afirka Kan Yin Tir Da Kisan Kare Dangin Isra’ila A Gaza
  • Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon
  • Trump Ya fadawa Turawa Kan Cewa Basa Cikin Tattaunawa Kan Tsagaita Wuta A Ukraine
  • Amurka Da Isra’ila Sun Sake Barazanar ‘Lugudan Wuta’ A Gaza