Ya ce Jihar Kogi ce ta gudanar da taron domin tana da shugabannin kungiyar a matsayin gwamna da mataimakinsa, inda ya ce Gwamna Usman Ododo na daya daga cikin jami’ansa a Jihar Neja sannan kuma mataimakin jami’in kungiyar malamai ta Nijeriya (NUT).

Ya ce, “Don haka muna son mu yi wannan taron ne domin mu saurare ku don sanin abin da aka yi da abin da ba a yi yadda ya kamata ba, don haka mu dauka mu kai musu.

“A gare mu, kamar zuwan gida ne. Muna so mu zo mu yi hulda da su don gano ko suna yin abubuwan da muke sukar wasu.”

Kan haramta kungiyoyin kwadago a kwalejojin jihar da gwamnatin baya ta Yahaya Bello ta yi kuwa, shugaban NLC ya nuna damuwa da cewa gwamnati ba ta da ikon haramta kungiyoyin da suke karkashin jeri na musamman na majalisa.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kungiyar Kwadago Matsin Rayuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira

Wata gobara da ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Munna Albadawi da ke ƙaramar hukumar Jere a Jihar Borno, ta lalata wasu gidaje 10 tare da salwantar da rayuwar yaro mai shekara 7 mai suna Abubakar Gargar.

A cewar shugaban sansanin, Babangida Mahmud gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 3:00 asubahin safiyar ranar 20 ga watan Maris, 2025, inda gobarar ta laƙume kayayyakin abinci da tufafi da dai sauran kayayyaki.

Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa ta mutu ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe

Wanda kawo yanzu ba a tantance adadin asarar da ta haifar ba baya ga salwantar rai guda.

Hukumar kashe gobara ta Jihar Borno tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro sun yi nasarar shawo kan gobarar da ƙyar da jibin goshi bayan da ta yi ɓarna mai yawan gaske.

Tuni dai aka yi wa marigayin jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya shimfiɗa.

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar (SEMA) da sauran hukumomin jin ƙai sun baza jami’ansu a sansanonin don daidaita lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i
  •  HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
  • Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
  • ’Yan adawa sun shirya ƙalubalantar Tinubu a zaɓen 2027 – Atiku
  • Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe
  • Wa Ke Dandana Kudar Matakin Harajin Kwastan Da Gwamnatin Amurka Ta Dauka
  • Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati