Gwamnatin Amurka Ta na Son Katse Dangantakan Da Ke Tsakanin Rasha Da Iran
Published: 16th, February 2025 GMT
Jakadan Amurka na musamman kan kasashen Rashad Ukraine ya bayyana cewa Amurka tana kokarin ganin ta kawo karshen dukkan dangantakar da ke tsakanin kasashen China da Rasha da kuma JMI.
Tashar talabijian ta Presstv a nan Tehran ta nakalto, Keith Kellogg ya na fadar haka a taron Munich na tsaro a jiya Asabar.
Ya kuma kara da cewa gwamnatin Trump tana aiki dare da rana don ganin ta wargaza dukkan dangantaka da ke tsakani Iran da Rasha da kuma China.
Jakadan ya kara da cewa dangantaka da ke tsakanin wadannan kasashen da JMI babu ita a shekaru 4 da suka gabata. Amma shugaba Donal Tromp yana aiki a kan haka. don ganin an katse dangantakar wadannan manya-manyan kasashe da JMI. Saboda barin Iran ita kadai.
Manufar dai ita ce tabbatar da cewa duk kasashen duniya sun maida Iran saniyar ware.
A sannan ne kuma takunkuman tattalin arziki mafi tsananin da gwamnatin Trump ta dorawa JMI zasu yi aiki. A sannan ne gwamnatin kasar Iran zata durkusar.
Kasar Iran dai tana da dangantaka ta musamman kuma masu dogon zango da wadannan kasashe biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora: Siyasar Kasar Iran Ta Ginu Ne Akan Kyautata Alaka Da Kasashen Makwabta
Jagoran juyin musulunci na Iran Ayatullah sayyid Ali Khamnei wanda ya gana da sarkin Katar a jiya Laraba ya bayyana cewa; Siyasar Iran ta ginu ne akan kyautata alaka da kasashen makwabta, kuma tuni an cimma sabbin matakai a wannan fagen.
Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma fada wa sarkin na Katar Tamim Bin Hamad ali-Sani cewa, ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci yana fadi tashi a wannan fagen na kyautata alaka da kasashen makwabta, tare da yin kira da cewa yarjeniyoyin da aka kulla su zama masu kare maslahar kasashen biyu.
Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya bayyana kasar Katar a matsayin kasa abokiya, kuma ‘yar’uwa ta Iran, duk da cewa har yanzu da akwai wasu batutuwa da ba a kai ga warware sub a,kamar dawo da kudaden Iran da aka zuba a Bankunan kasar daga Korea Ta Kudu.
A nashi gefen sarkin Katar ya jinjinawa matakan da Iran din take dauka na taimakawa raunana a duniya, da kuma al’ummar Falasdinu, kuma yadda ta kasance a tare da Falasdinawa wani abu ne da ba za taba mancewa da shi ba har abada.