HausaTv:
2025-02-20@08:56:01 GMT

Guterres Ya Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Sudan

Published: 16th, February 2025 GMT

Babban sakataren MDD Antonio Guterres  wanda ya halarci taron kungiyar tarayyar Afirka AU da aka bude a birnin Addis Ababa na kasar Habasha, ya kira yi kungiyoyin kasa da kasa da su kai daukin gaggawa ga kasar Sudan ta fuskar bada kayakin agaji.

Guterres ya nanata muhimmancin kai kayakin abinci da sauran kayakin da ake bukatuwa da su, domin taimakawa mutanen kasar ta Sudan da yaki ya daidaita.

Babban magatakardar MDD ya yi ishara da rawa ta jarunta da kungiyoyin mata  suke yi a cikin yanayi mai hatsari,tare dayin kira da a kare rayukan fararen hula.

Har’ila yau ya yi kira da a kawo karshen shigar da makamai zuwa kasar ta Sudan da bai wa zaman lafiya dama, a cikin watan Azumin Ramadana mai shigowa.

A mako mai zuwa ne dai MDD za ta kaddamar da gidauniyar agaji ta neman kudaden da za su kai dala biliyan 6 domin taimakawa miliyoyin mutanen Sudan da suke zaman hijira a kasashe makwabta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne

A ranar 15 ga watan Fabrairu, ministocin harkokin waje na kasashen Amurka, Japan, da Koriya ta Kudu sun yi shawarwari a Munich na kasar Jamus. A cikin sanarwar hadin gwiwar da suka fitar, a karon farko, sun bayyana goyon bayansu ga yadda Taiwan za ta shiga cikin kungiyoyin kasa da kasa da suka dace, tare da jaddada muhimmancin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun Taiwan. Dangane da wannan batu, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Guo Jiakun, ya sake nanata cewa, Taiwan wani bangare ne na kasar Sin da ba za a iya raba shi da ita ba, kuma batun Taiwan lamari ne na cikin gidan kasar Sin kawai, kuma ba ta yarda da wata tsangwama daga waje ba. Shigar Taiwan cikin ayyukan kungiyoyin kasa da kasa dole ya kasance bisa ka’idar Sin daya tak a duniya. A ko da yaushe kasar Sin tana adawa da yadda wasu kasashe ke hada kai wajen kafa kananan kungiyoyi, da tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasar Sin, tare da suka da bata wa kasar Sin suna, da tayar da husuma da adawa, kana ta mika wa kasashen da abin ya shafa gamsasshen korafi.

Bugu da kari, a matsayin martani ga kwaskwarimar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta yi kan takardar sahihancin bayanai kan dangantakar Amurka da Taiwan, Guo Jia Kun ya bukaci bangaren Amurka da ya gaggauta gyara kuskuren, da kuma mutunta ka’idar Sin daya tak da sanarwoyi guda uku na Sin da Amurka, kuma ta bi a hankali wajen tinkarar batun Taiwan. (Mohammed Yahaya)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  •  Jagora: Siyasar Kasar  Iran  Ta Ginu Ne Akan Kyautata Alaka Da Kasashen Makwabta
  • Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno
  • Sojojin Sudan Sun Killace Fadar Shugaban Kasa Da Take A Hannun ‘Yan Tawayen A Birnin Khartum
  • Kasashen Rasha Da Amurka Sun Kuduri Anniyar Kawo Karshen Yaki A Ukraine
  • Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata
  • Kasar Iran Zata Aika Da Tawaga Mai Karfi Zuwa Jana’izar Sayyid Nasarallah
  • Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne
  • FG Ta Jaddada Bukatar Samarda Sabbin Ka’idojin Visa Domin Taimakawa Kasuwancin A Duniya
  • Trump Ya fadawa Turawa Kan Cewa Basa Cikin Tattaunawa Kan Tsagaita Wuta A Ukraine