HausaTv:
2025-03-23@03:58:30 GMT

Guterres Ya Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Sudan

Published: 16th, February 2025 GMT

Babban sakataren MDD Antonio Guterres  wanda ya halarci taron kungiyar tarayyar Afirka AU da aka bude a birnin Addis Ababa na kasar Habasha, ya kira yi kungiyoyin kasa da kasa da su kai daukin gaggawa ga kasar Sudan ta fuskar bada kayakin agaji.

Guterres ya nanata muhimmancin kai kayakin abinci da sauran kayakin da ake bukatuwa da su, domin taimakawa mutanen kasar ta Sudan da yaki ya daidaita.

Babban magatakardar MDD ya yi ishara da rawa ta jarunta da kungiyoyin mata  suke yi a cikin yanayi mai hatsari,tare dayin kira da a kare rayukan fararen hula.

Har’ila yau ya yi kira da a kawo karshen shigar da makamai zuwa kasar ta Sudan da bai wa zaman lafiya dama, a cikin watan Azumin Ramadana mai shigowa.

A mako mai zuwa ne dai MDD za ta kaddamar da gidauniyar agaji ta neman kudaden da za su kai dala biliyan 6 domin taimakawa miliyoyin mutanen Sudan da suke zaman hijira a kasashe makwabta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana a jiya cewa, kasar Sin na dora muhimmanci sosai kan hadin gwiwar dake tsakanin kasarsa da kasashen Japan da Koriya ta Kudu, kuma tana da kwarin gwiwa kan hakan.

Wang ya bayyana hakan ne a lokacin da yake halartar taron firaministan kasar Japan Shigeru Ishiba a birnin Tokyo tare da ministocin harkokin wajen kasashen Japan da Koriya ta Kudu. Yana mai cewa, an fara hadin gwiwa tsakanin Sin da Japan da Koriya ta Kudu da wuri, inda aka samu sakamako da dama, kuma tana da babban tasiri, wadda ta taka muhimmiyar rawa wajen inganta fahimtar juna da hadin gwiwar moriyar juna a tsakaninsu.

Wakilin Musamman Na Xi Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugabar Namibiya Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024 

Kazalika, dangantakar Sin da Japan da Koriya ta Kudu tana kara bunkasa, za a kara tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin. Bugu da kari, hadin gwiwarsu na kara zurfafa, kasashen yankin za su kara kaimi wajen tunkarar kalubale daban daban daga waje.

Wang ya kara da cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasar Japan da Koriya ta Kudu, wajen kafa sahihiyar ra’ayi game da tarihin yakin duniya na biyu, da kiyaye tsarin bangarori daban daban, da kiyaye muhimmiyar rawar da MDD ke takawa a tsarin kasa da kasa, da ci gaba da inganta hadin gwiwa, da ba da gudummawa ga samun zaman lafiya da wadata a shiyyar da duniya baki daya. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar
  • Cibiya Mai Fafutukar Kare Hakkokin Falasdinawa “Global 195” Ta Shelanta Farautar Sojojin HKI Da Su KaTafka Laifukan Yaki
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
  • Sin: Shingayen Kasuwanci Suna Illata Wadatar Tattalin Arzikin Duniya
  • Manufofin Kasar Sin Sun Zamo Jagora Ga Duniya A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama
  • Iran: Jagora ya yi kira da a karfafa dogaro da kai a cikin gida domin dakile tasirin takunkumai
  • OIC ta yi Allah wadai da sake dawo da hare-haren yahudawan sahyuniya a kan a zirin Gaza
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu
  • A Jiya Laraba Ce Iran Take Bukukuwan Cika Shekaru 78 Da Kwatar Kamfanin Man Fetur Na Kasar Daga Hannun Turawan Burtaniya