Trump Ya Bukaci Ukirain Ta Bada Ma’adinanta Ga Kasar Amurka Idan Tana Son Ta Taimaka Mata Da Kayakin Yaki
Published: 16th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce, Amurka ta na son mallakar ma’adanan na kasar Ukiraniya, wadadensu ya kudadensu ya kai dalar Amurka biliyan 500, a matsayin mayar da kwaryar taimakon Amurkan ta fuskar soja da makamai.
A wata hira da tashar talabijin ta “FOX NEWS” ta yi da shi, shugaban kasar ta Amurka Donald Trump ya ce, ya na son Amurka ta mallaki ma’anadai na kasar Ukiraniya a matsayin ladar da tallafin sojen da take bukata daga Amurka.
Gwamnatin Donald Trump ta gabatar wa da Kiev shawarar yin musayar ma’adanai na musamman da irinsu sun yi karanci a duniya, da take da su, na kaso 50% da hakan zai zama abinda take biyan Amurka da su, madadin taimakon soje da take samu daga wajenta.
Sakataren Biatul-Malin Amurka Scott Bessent ne, ya gabatarwa da shugaban kasar Ukiraniya Volodymir Zeleski shawarar hakan a wata ganawa da su ka yi a ranar Larabar da ta gabata a birkin Kiev.
A karkashin wannan shawarar Amurkan za ta aike da sojojinta domin bada kariya ga wuraren hako wadannan ma’adanan a gabashin turai.
Tashar talabijin ta NBC da ta watsa wannan labarin ta kuma ambato cewa, shugaban kasar ta Ukiraniya ya ki rattaba hannu akan yarjejeniyar ya kara da cewa, zai tuntubi jami’an gwamnatin kasar sa kafin haka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati ta kashe N5bn domin bai wa mata tallafin kiwon awakai a Katsina
Gwamnatin Katsina ta kashe kimanin Naira biliyan 5.4 domin bai wa mata 3,610 tallafin kiwon awakai.
Gwamna Dikko Umar Radda ne ya bayyana hakan a yayin ƙaddamar da shirin raba tallafin awakan a gundumar Dan-Nakolo da ke Ƙaramar Hukumar Daura ta jihar.
Ya bayyana cewa, a ƙarƙashin shirin, an raba wa mata 3,610 awakai huɗu-huɗu a gundumomi 361 da ke faɗin jihar.
Gwamnan ya bayyana cewa wannan shiri wani ginishiki ne na bunƙasa harkokin noma da kiwo wanda yake da burin ganin Katsina ta zama ja gaba a fannin dogaro da kai a Arewacin Nijeriya da ma ƙasar baki ɗaya.
A cewar Gwamnan, kiwon awakai yana da muhimmanci kuma ɗaya ne daga cikin muradin gwamnantinsa na bunƙasa harkokin noma da kiwo da wadatar abinci sannan kuma abin dogaro da kai ga ƙananan manoma.
A nasa jawabin, mashawarcin gwamnan ma musamman kan harkokin kiwo, Suleiman Yusuf, ya ce bai wa mata tallafin awakai babbar hujja kan yadda gwamnatin ke ƙoƙarin ganin ta rage talauci a tsakanin al’umma.
“Mun ƙaddamar da wannan shiri ne saboda fahimtar da muka yi wa muhimmacin da rawar da mata suke takawa wajen bunƙasar tattalin arziki.
“Saboda haka wannan tallafi aka bai wa matan muna da yaƙinin cewa zai kawo kyakkyawan sauyi a tsakanin al’umma,” in ji Yusuf.