Hizbullah Ta Ce Bata Son Amurka Da HKI Su yi Shishigi Cikin Al-Amuran Cikin Gida Na Kasar Lebanon
Published: 16th, February 2025 GMT
A wani zanga-zangar lumana da suka gabatar a jiya Asabar masu goyon bayan kungiyar Hizbullah sun yi kira ga gwamnatin kasar Lebanon kada ta bari Amurka da HKI su zama su ne ke jajjuya al-amuran kasar.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Mahmood Qamati shugaban kwamitin siyasa na kungiyar Hizbullah ya na fadar haka a jiya Asabar, a kan babban titin da ya ke zuwa tashar jiragen sama na birnin Beirut babban birnin kasar kasar, wato Rafiqul Hariri INT.
Qamati ya kara da cewa bai kamata HKI tayiwa jiragen saman Iran masu zuwa beiru barazana, sannan ita kuma gwamnatin kasar Lebanon ta hana jiragen Iran sauka a Lebanon ba.
Kafin haka dai, HKI ta yi barazanar kakkabo dukkan jiragen fasinja masu zuwa kasar Lebanon don suna kawowa kungiyar Hizbullah makamai ko kudide.
Sannan maimakon gwamnatin kasar Lebanon ta san yadda zata yi ta tabbatar HKI al-amarin ba haka ba. Ta kare kasar Iran sai ta dakatar da dukkan jiragen fasinja masu zuwa Beirut daga Iran don wai kada HKI ta kakkabosu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
Kasashen Iran da Hadaddiyar Daular Larabawa sun bayyana matukar damuwarsu kan yadda gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta sake dawo da yakin kisan kare dangi a zirin Gaza da kuma hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen.
A wata tattaunawa ta wayar tarho a wannan Juma’a, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da takwaransa na UAE Abdullah bin Zayed Al Nahyan, sun tattauna batutuwan da suka shafi yankin, musamman ma ayyukan wuce gona da iri na Isra’ila a Gaza da kuma hare-haren Amurka a Yemen.
Araghchi ya yi kakkausar suka kan kisan gillar da gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta yi wa daruruwan Falasdinawa da ba su ji ba ba su gani ba tun daga ranar Talata, yana mai jaddada cewa yin hakan saba yarjejeniyar tsagaita bude wuta ne da aka rattaba hannu a kansa.
Ya kuma yi Allah wadai da hare-haren da sojojin Amurka ke ci gaba da kai wa kasar Yemen, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mata da kananan yara da dama, tare da lalata muhimman ababen more rayuwa na yankin, da kuma jefa mutane cikin kangin talauci da yunwa.
Araghchi ya kara da cewa, laifuffukan da gwamnatin yahudawan sahyoniya ke aikatawa a Gaza da kuma harin da Amurka ta kai kan kasar Yaman na bukatar daukar matakin gaggawa da hadin gwiwa daga kasashen yankin da kum akasashen musulmi, domin dakatar da wannan ta’addanci da ke ci gaba da kawo rashin tsaro a duk fadin yankin gabas ta tsakiya.
A nasa bangaren, Ministan kasar UAE Abdullah bin Zayed ya bayyana matukar damuwarsa kan tabarbarewar al’amura a yankin, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin damuwa matuka.
Ya jaddada bukatar ci gaba da tuntubar juna tsakanin kasashen yankin domin hana ci gaba da tabarbarewar zaman lafiya.
Rahotanni sun tabbatar da cewa sojojin Isra’ila sun zafafa kai hare-hare ta sama da kuma ta kasa a zirin Gaza tun daga ranar Talata, inda suke kai hari kan wuraren zaman jama’a da hakan ya hada da wuraren da aka tsugunnar da dubban mutane da suka rasa muhallansu da kuma gidaje, gami da asibitoci, tare da hana duk wasu ayyuka na jin kai ko ceton jama’a ko kai daukin gaggawa.