A wani zanga-zangar lumana da suka gabatar a jiya Asabar masu goyon bayan kungiyar Hizbullah sun yi kira ga gwamnatin kasar Lebanon kada ta bari Amurka da HKI su zama su ne ke jajjuya al-amuran kasar.

Tashar talabijan ta Presstv  a nan Tehran ta nakalto Mahmood Qamati shugaban kwamitin siyasa na kungiyar Hizbullah ya na fadar haka a jiya Asabar, a kan babban titin da ya ke zuwa tashar jiragen sama na birnin Beirut babban birnin kasar kasar, wato Rafiqul Hariri INT.

Airport, inda mabiya kungiyar suka yi gaggami, don nuna rashin amincewar da hana jiragen saman Iran sake sauka a tasahar.

Qamati ya kara da cewa bai kamata HKI tayiwa jiragen saman Iran masu zuwa beiru barazana, sannan ita kuma gwamnatin kasar Lebanon ta hana jiragen Iran sauka a Lebanon ba.

Kafin haka dai, HKI ta yi barazanar kakkabo dukkan jiragen fasinja masu zuwa kasar Lebanon don suna kawowa kungiyar Hizbullah makamai ko kudide.

Sannan maimakon gwamnatin kasar Lebanon ta san yadda zata yi ta tabbatar  HKI al-amarin ba haka ba. Ta kare kasar Iran sai ta dakatar da dukkan jiragen fasinja masu zuwa Beirut daga Iran don wai kada HKI ta kakkabosu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Za Ta Aike Da Tawaga A Matakin Koli Don Halartar Jana’izar Nasrallah

Iran ta bayyana cewa za ta aike da tawaga a matakin koli zuwa jana’izar mirigayi babban sakataren kungiyar Hizbollah ta kasar Lebanon Hassan Nasrallah.

Da yake sanar da hakan kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei ya ce kasar za ta halarci gagarumin bikin mai matukar muhimmanci,

Tunda farko dai kungiyar gwagwarmayar Hizbullah ta kasar Lebanon ta sanar da cewa tawagogin kasashe 79 za su halarci bikin tunawa da marigayi babban sakataren kungiyar Sayyid Hassan Nasrallah da kuma shugaban majalisar zartarwarta Sayyid Hashem Safieddine.

Sheikh Ali Daher, kodinetan babban komitin jana’izar Nasrallah da Safieddine, ya bayyana cewa bikin da aka shirya yi a ranar 23 ga watan Fabrairu, zai kasance “ranar tunawa da shugaban wanda aka zalunta a kan ma’abuta girman kai, da kuma shahidan bil’adama a kan mulkin mallaka”.

Ya kara da cewa jana’izar za ta ci gaba da zaburar da mutane masu ‘yanci a duniya shekaru da dama masu zuwa.”

Daher ya yi nuni da cewa bikin zai dauki kimanin sa’a daya kuma zai hada da jawabin babban sakataren kungiyar Sheikh Naim Qassem.

Sayyid Nasrallah ya yi shahada ne a yayin harin bam da Isra’ila ta kai a kudancin birnin Beirut a ranar 27 ga Satumba, 2024, Shi kuwa Safieddine ya yi shahada a lokacin harin da Isra’ila ta kai a watan Oktoban 2024.

Kungiyar Hizbullah ta dage bikin jana’izar shugabannin biyu saboda fargabar hare-haren Isra’ila a yayin bikin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Kwalejin Koyon Tukin Jiragen Sama
  • Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan
  •  Rasha Ta Kakkabo Jiragen  Sama Marasa Matuki 9 Na Kasar Ukiraniya
  • Kasar Iran Zata Aika Da Tawaga Mai Karfi Zuwa Jana’izar Sayyid Nasarallah
  • Sojojin HKI Sun Fara Ficewa Daga Wasu Wurare A Kudancin Kasar Lebanon
  • Janye Tallafin Amurka Ya Jefa Masu Fama Da Cutar HIV A Kasar Afirka Ta Kudu Cikin Fargaba
  • Hamas Ta Sanar Da Shahadar Wani Jagoranta Da HKI Ta Kashe A Lebanon
  • Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne
  • Iran Za Ta Aike Da Tawaga A Matakin Koli Don Halartar Jana’izar Nasrallah
  • HKI Ba Zata Yarda A Kafa Kasar Palasdinu Ba, Saboda Barazana Ce Ga Wanzuwar HKI