Aminiya:
2025-04-13@09:52:24 GMT

Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 a Borno

Published: 16th, February 2025 GMT

Ƙungiyar Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan takwararta na ISWAP da dama yayin wani ƙazamin rikici da suka tafka ranar Juma’a a Ƙaramar Hukumar Kukawa da ke Jihar Borno.

Bayanai sun ce an kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 yayin harin da mayaƙan Boko Haram suka kai ƙarƙashin jagorancin wani ta’adda mai suna Bakoura.

Dalilin da ’yan siyasa ke sauya sheƙa zuwa APC — Tambuwal Ɗan Nijeriya ya lashe kyautar Kundin Bajinta na Duniya a fagen ɗaukar hoto

Wata majiya ta shaida wa ƙwararren mai sharhi kan yaƙi da tayar da ƙayar baya, Zagazola Makama, cewa yaƙin da aka fara tun da sanyin safiyar ranar 14 ga watan Fabrairu ya haɗa da sansanonin ISWAP da ke Toumbun Gini da Toumbun Ali.

Mayaƙan Boko Haram, waɗanda rahotanni suka ce sun ragargaji sansanin na ISWAP  a wani ƙazamin faɗan ya ɗauki tsawon yini guda ana gwabzawa.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa an kashe wasu manyan kwamandojin ISWAP musamman ‘yan kabilar Buduma a yayin harin.

A cewar majiyar, daga cikin ’yan ta’addan ISWAP da aka kashe sun haɗa da wasu manyan-manyan kwamandojin da ake kyautata zaton sun taka rawa wajen kisan kiyashin da aka yi wa manoma da dama a Kukawa a tsakanin 12 zuwa 13 ga watan Janairu na wannan shekara ta 2025.

Majiyar ta ce mayakan Boko Haram sun yi wa kungiyar ta ISWAP asara mai yawa bayan da suka mamaye sansaninsu, inda suka ƙwace makamai da kayan aiki.

A wani yunƙuri na faɗaɗa hare-haren nasu, an ce mayaƙan na Boko Haram daga tsibirin Bokorram sun ɗaura ɗamara domin tunkarar mayaƙan ISWAP a Gemu da Mallam Karamti.

Zagazola ya bayyana cewa akwai yiwuwar ana gab da samun ƙarin fadace-fadace, musamman a Ƙaramar Hukumar Kukawa, yayin da mayaƙan Boko Haram ke ƙara ƙaimi wajen yaƙar ISWAP.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP jihar Borno da mayaƙan

এছাড়াও পড়ুন:

Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari a Kaduna.

Atiku ya samu rakiyar tsofaffin gwamnoni da suka haɗa da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal da wasu jiga-jigan ’yan siyasa.

An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji

Kamar yadda aka wallafa bidiyon ziyarar a Shafin Atiku na Facebook, an rubuta cewa sun ziyarci Buharin, kuma sun sha dariya.

“A matsayina na Wazirin Adamawa, na tsaya domin gudanar da shagungulan Sallah a Adamawa, inda na wakilci Sarkin Adamawa, Lamiɗo Fombina a wasu shagulgulan.

“Yau kuma na kai ziyarar gaisuwar Sallah ga Muhammadu Buhari wanda ya shugabanci ƙasar a tsakanin 2015 zuwa 2023. Na ji daɗin ziyarar, saboda kamar yadda ya saba, ya yi ta ba mu dariya sai da haƙarƙarina suka yi zafi.” Cewar Atiku.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bam Ya Hallaka Mutane 8, Wasu da Dama Sun Jikkata A Borno
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno
  • ‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Mamaye Sassan Jihar Borno -Zulum
  • Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari
  • Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji
  • Za a mayar da tubabbun ’Yan Boko Haram cikin al’umma – Gwamna Buni