Yadda za a yaƙi talauci a Arewa maso Gabas — Shettima
Published: 16th, February 2025 GMT
Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya buƙaci Hukumar Bunƙasa Arewa maso Gabas (NEDC) da ma’aikatar raya yankuna ta tarayya da su magance talauci a yankin ta hanyar zuba jari a fannin ilimi.
Shettima ya yi wannan kiran ne a yayin wata ganawa da ya yi da mahukuntan hukumar ta NEDC a fadar shugaban kasa da ke Abuja, inda suka yi masa bayani kan wani shiri na harkokin ilimin babbar sakandare — ASSEP.
Ya kuma yaba wa hukumar NEDC kan yadda ta ke ba da gudummawar a fannin ilimi, inda ya ce za a riƙa tunawa da irin wannan ƙoƙari a nan gaba.
Shettima ya kuma yi nuni da cewa, akwai matsanancin talauci a yankin Arewa maso Gabas, inda ya kwatanta shi da wasu yankunan da ke fama da talauci a duniya, yana mai alakanta bullar ƙungiyoyin tsageru a yankin da irin waɗannan yanayi na zamantakewa.
Duk da kalubalen, ya yaba wa hukumar ta NEDC da abokan huldar ta, ciki har da Dokta Mariam Masha, saboda aikin da suke yi na inganta shirin ASSEP, yana mai cewa akwai yiwuwar canza yanayin yankin.
Mataimakin shugaban ƙasar ya buƙaci hukumar NEDC, ma’aikatar raya yankuna, da sauran masu ruwa da tsaki da su haɗa kai don samun ingantaccen aiki da samun nasara wajen aiwatar da shirin na ASSEP.
A nasa ɓangaren, Ƙaramin Ministan ci gaban yankin, Uba Ahmadu, ya lura cewa shirin na ASSEP na da zummar inganta ilimin sakandare a yankin, tare da ajandar Shugaba Bola Tinubu na inganta matakan ilimi na ƙasa.
Manajan Daraktan Hukumar NEDC, Alhaji Mohammed Alkali, ya yi cikakken bayanin dangane irin ƙoƙarin da hukumar ke yi wajen bunƙasa rayuwar bil’adama, ciki har da horar da malamai da kafa cibiyoyin ilimin yanar gizo (ICT) a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
Babban sakataren kungiyar kasashen Larabawa na yankin tekun Farisa (PGCC) ya yi fatan alkhairi ga kasashen Iran da Amurka a tattaunawa ba kai tsaye ba a tsakaninsu dangane da shirin Nukliya ta kasar Iran na zaman lafiya wanda suka fara, a birnin Mascat na kasar Omman a ranar Asabar da ta gabata.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Jasem Mohamed AlBudaiw yana fadar haka a jiya Lahadi ya kuma kara da cewa, kungiyar tana bukatar gidan an warware matsaloli tsakanin kasashen duniya ta hanyar tattanawa. Haka ma tsakanin kasashen yankin.
AlBudaiw ya yabawa kasar Omman da shirya wannan tattaunawar, sannan ya yi fatan tattaunawan da aka fara zai kai ga rage tada jijiyoyin wuya a yankin da kuma kasashen duniya, ya kuma ce kasashen yankin suna fatan zasu kai ga sakamako mai kyau tsakanin kasashen biyu.
Gwamnatin kasar Iran dai tana har yanzun suna shakkar kasar Amurka saboda yawan yaudarar da tayiwa kasar a baya. Musamman fitar kasar daga yarjeniyar JCPOA a shekara ta 2018. Da kuma yawan takunkuman da ta dorawa a kasar tun lokacin.
Daga karshe babban sakataren kungiyar ta PGCC ya ce tana fatan za’a kawo karshen duk wani rikici a gabas ta tsakiya daga ciki har da na HKI a falasdinawa a Gaza ta hanyar tattaunawa da fahintar Juna.