Aminiya:
2025-02-20@08:55:52 GMT

Mazabar Tsanyawa/Kunchi ta shafe shekara guda ba tare da wakilci ba

Published: 16th, February 2025 GMT

Shekara guda bayan da Hukumar Zabe (INEC) ta dakatar da sake zaben mazabar Tsanyawa da Kunci a Majalisar Dokokin Jihar Kano, yankin ya ci gaba da zama babu zaɓaɓɓen wakili da yake wakiltar su a Majalisar Dokokin jihar.

Hukumar Zabe ta Ƙasa ta dakatar da sake zaɓen ne a ranar 3 ga Fabrairu, 2024, bayan da wasu da ake zargin ’yan bangar siyasa ce suka tarwatsa sake gudanar da zaben a wasu rumfunan zabe da dama a kananan hukumomin biyu.

Yadda za a yaƙi talauci a Arewa maso Gabas  — Shettima Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 a Borno

A shekarar 2023 ce Kotun Daukaka kara ta soke zaben dan Majalisar Dokoki na Jam’iyyar APC mai wakiltar mazabar, Alhaji Garba Ya’u Gwarmai, biyo bayan kalubalantar nasarar da ya samu a shari’a da Alhaji Yusuf Ali Maigado na Jam’iyyar NNPP ya shigar.

Kotun ta bayar da umarnin a sake yin zabe cikin kwanaki 90.

Da yake tsokaci kan rashin wakilcin da mazabar ta daɗe ba ta da shi, masanin harkokin siyasa, Dokta Kabiru Sufi ya ɗora alhakin lamarin ga Hukumar Zabe ta kasa da kuma ’yan siyasa da masu ruwa da tsaki daga mazabar, yana mai zargin su da gazawa wajen ganin an gudanar da zaben cikin lumana da kwanciyar hankali.

“Masu ruwa da tsaki a yankin suna da hujjar tambayar Hukumar Zabe ta kasa dalilin da ya sa ta gaza kammala aikin gudanar da zaben kamar yadda doka ta tanada,” in ji Dokta Sufi.

Wani mazaunin yankin Malam Muhammad Tsamiya ya koka da rashin samun wakilci, inda ya bukaci gwamnan jihar da ya tabbatar da cewa ba a yi watsi da mazabar ba, musamman ganin yadda take fama da rashin isassun kayayyakin more rayuwa.

“Kunci yanki ne mai nisa, inda hatta malaman da aka tura domin gudanar da aikin nan sun ki zuwa saboda ba mu da hanyoyi ga matsalar ruwan sha da dai sauran matsaloli.

“Don haka a siyasance, gwamna shi ne wakilinmu tun da jihar baki ɗaya mazabarsa ce,” inji shi.

Ya zuwa yanzu dai Hukumar Zabe INEC ba ta sanar da wata rana ba da za a sake gudanar da zaben ba.

Da wakilinmu ya tuntubi shugabar kula da sashen wayar da kan masu kada kuri’a ta Hukumar Zabe ta Kasa, Hajiya Safiya ta bayyana cewa, idan hukumar ta shirya lokacin gudanar da zaben, kwamishinan Hukumar Zabe ta kasa, Ambasada Abdu Zango zai kira taron masu ruwa da tsaki domin tattauna tsare-tsaren yadda za a gudanar da zaɓen.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Zaɓe gudanar da zaben Hukumar Zabe ta

এছাড়াও পড়ুন:

Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara

Wani sabon rikici ya sake kunno kai a tsakanin manyan jam’iyyun siyasa biyu a Jihar Zamfara.

Rigimar wadda ta kunno tsakanin APC da PDP ta samo asali ne tun bayan da wasu matasa suka yi yunƙurin hana wani taro na ɗan Majalisar Wakilai da za a gudanar a garin Maru.

Mutum 10 sun rasu, an lalata dukiyar N11bn yayin zanga-zangar yunwa a Kano — Rahoto Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno

Hakan ya sa Gwamnatin Zamfara ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal ta ɗauki wani matakin da take ganin zai kawo lafawar lamarin.

Sai dai kuma matakin da gwamnatin ta ɗauka bai yi wa jam’iyyar APC daɗi ba, inda ta nuna rashin gamsuwa tare da zargin ba a yi mata adalci ba saboda kasancewarta jam’iyyar adawa.

A bayan nan ne Gwamnatin Zamfara ta dakatar da duk wasu tarukan siyasa a jihar saboda samar da zaman lafiya da daidaito.

A bayanin da mai taimaka wa Gwamnan Zamfara kan kafafen yaɗa labarai, Mustapha Jafaru Kaura ya fitar, ya ce matakin na zuwa ne bayan hatsaniyar da aka samu a tsakanin jam’iyyun PDP da APC a Ƙaramar Hukumar Maru.

“Duk wani taron siyasa da zagaye an dakatar da shi a wannan lokaci, la’akari da abin da ya faru a Maru inda aka samu salwantar rayuka da ƙone-ƙonen dukiya.”

Hadimin gwamnan ya ce an ɗauki matakin ne ba don a musguna wa wasu ba face sai don samar da zaman lafiya kuma dokar da aka sanya ta wucin gadi ce.

Jam’iyyar APC a Zamfara ta nuna rashin gamsuwar ta kan matsayar da gwamnatin ta ɗauka tana mai zargin cewa gwamnatin ta mayar da hankali kan abin da ba shi ne ya fi ba.

Wata sanarwa da APC ta fitar ta bayyana cewa dole ne hukumar ’yan sanda a jiha ta kama waɗanda suka kai farmaki ga magoya bayanta a yayin da suke gudanar da kowane taro.

Jam’iyyar ta ce gargaɗin ya zama wajibi ganin yadda ‘yan sanda suka fita batun koken da aka gabatar musu a rubuce har guda uku.

“A cikin matasan da muke zargi, ’yan bangar siyasa daga jam’iyyar PDP da ’yan sa kai ne suka kawo farmaki a wurin rabon kayan ɗan Majalisar Wakilai na Maru da Bungudu, Honarabul Abdulmalik Zubairu Bungudu.

“Ɓatagarin sun laɓe ne kan hanyar Gusau zuwa Bungudu inda suka kai harin kan magoya bayan APC sannan suka lalata ababe hawa da dama.

Sakataren yaɗa labarai na APC a Zamfara, Yusuf Idris Gusau ya yi tir da lamarin, yana mai kiran jami’an tsaro su ɗauki matakin gaggawa.

Idris Gusau ya ce “muddin ba haka ba zai sa mu riƙa kare kansu kan kowane mutum da ya nemi cin zarafinsu.”

Sakataren ya nemi magoya bayansu da su kwantar da hankali domin za a tabbatar da an yi adalci ga waɗanda aka ji wa rauni ko aka ɓarnata dukiyoyinsu.

“A matsayinmu na masu son zaman lafiyar Jihar Zamfara ba za mu bari a yi amfani da mu don kawo hargitsi ba kamar yadda jam’iyyar PDP ke kitsawa,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Bayyana Ra’ayin Sin Kan Yadda Za A Karfafa Huldar Cude-Ni-In-Cude-Ka A Duniya
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan
  • Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara
  •  Rasha Ta Kakkabo Jiragen  Sama Marasa Matuki 9 Na Kasar Ukiraniya
  • AU Ta Zabi Sabbin Shugabanni Ana Tsaka Da Tashe-tashen Hankula A Nahiyar
  • Kasar Sin Ta Taya Mahmoud Ali Youssouf Murnar Zabarsa Da Aka Yi A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Gudanarwar AU
  • Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Yobe
  • Hukumar Kula Da Ayyukan Duba-gari Ta Kasa Za Ta Karrama Shugaba Tinubu 
  • Yadda na yi wa budurwar da muka haɗu a Facebook gunduwa-gunduwa —Matashi