HausaTv:
2025-03-23@08:40:00 GMT

Fararen Fatar Kasar Afirka Ta Kudu Sun Yi  Gangamin  Nuna  Goyon Bayan Trump

Published: 16th, February 2025 GMT

A jiya Asabar ne da wasu kungiyoyi na fararen fata a kasar Afirka ta kudu sun yi  gangami a bakin ofishin jakadancin Amurka dake birnin Pretoria suna masu nuna goyon bayansu ga kalaman da Donald Trump  da ya riya cewa, gwamnatin kasar da bakaken fata masu rinjaye tana nunawa fararen fata wariya.

Daruruwan masu gangamin sun daga kwalaye da aka yi rubuta a jikinsu da su ka kunshi yin godiya ga Donald Trump da ya yi Magana akan abinda ce, damuwarsu ce.

Wanda ya  shirya gangamin Willem Petzer, ya  ce, yana son fadawa kasashen turai cewa,  suna da kawaye a cikin kasar Afirka ta kudu.

Da dama daga cikin mahalarta gangamin sun fito ne daga al’ummar Afirkana da Trump ya ce, gwamnatin kasar ta yi dokar kwace musu filaye.

Shi kuwa Heinrich Steinhausen ya bayyana cewa; A cikin shekaru 30 na bayan nan an sami rabuwar kawuna a cikin kasar saboda abinda ya kira siyasar gwamnati.

Tuni dai gwamantin kasar Afirka ta kudu ta yi watsi da wadannan zarge-zargen na Donald Trump.

Masu bin diddigin abinda yake faruwa suna ganin cewa Amurkan tana yin matsin lamba ne akan kasar Afirka ta kudu saboda ta shigar da kasar “Isra’ila” a gaban kotun duniya ta manyan laifuka da ta yanke hukunci akan Isra’ila da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Afirka ta kudu

এছাড়াও পড়ুন:

Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa

A kwanan nan ne sakatare janar na kungiyar ASEAN Kao Kim Hourn ya bayyana a wata hirar da ya yi da wakilin babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin na CMG cewa, nasarorin da Sin ta samu ta fuskar ci gaba ba sakamakon ‘siddabaru’ ba ne, illa sakamakon aiki tukuru kuma mai dorewa.

Kao Kim Hourn, wanda ya ziyarci kasar Sin sau da dama, ya yi tsokaci kan abubuwan da ya gani a wadannan ziyarce-ziyarcensa. Ya bayyana cewa, tafiya daga filin jirgin sama zuwa tsakiyar gari, ya shaida yadda kasar Sin take da tsabta, da koren muhalli, da tsaro, da duk sakamakon ci gabanta na zahiri. Abin ban mamaki ne ganin yadda kasar Sin ta canza a cikin ‘yan shekarun nan. Abubuwan da ya gani a kasar Sin a cikin ‘yan shekarun nan sun matukar bambanta da abubuwan da ya gani lokacin da ya ziyarci kasar Sin a shekarun 1990.

Ya jaddada cewa, irin wadannan sauye-sauyen na nuna gagarumin kokari na bayan fage. Kana samun ci gaba yana bukatar aiki tukuru. Kao ya bayyana cewa, ci gaban da kasar Sin ta samu ne ba ta hanyar siddabaru ba, ta samu ne a sakamakon namijin kokarin da shugabannin kasar Sin da jama’arta suka yi. Ya kuma kara da cewa, ci gaban kasa yana bukatar kuzari mai yawa, da nagartaccen jagoranci, da dimbin albarkatu, da jajircewar al’ummarta. Kasar Sin misali ce ga hakan. (Mohammed Yahaya)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  
  • Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa
  •  Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar
  • An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar
  • An gudanar da gagarumar zanga-zangar nuna goyon bayan Falastinu a kasar Jordan
  • Ba Na Goyon Bayan Dakatar Da Gwamnan Jihar Ribas – Ndume
  • Wa Ke Dandana Kudar Matakin Harajin Kwastan Da Gwamnatin Amurka Ta Dauka
  • Kungiyar M-23 Ta Kasar Kongo Ta Kara Nusawa Gaba A Don Mamaye Karin Yankuna A Gabacin Kongo