Sojojin HKI Suna Cigaba Da Kai Hare-hare A Yankin Tulul-Karam
Published: 16th, February 2025 GMT
Sojojin mamayar HKI suna cigaba da kai hare a yankin Tul-Karam da sansanonin ‘yan gudun hijira da suke cikinta wanda ya dauki kwanaki 21 suna yi.
Bugu da kari, sojojin mamayar suna cigaba da kama Falasdinawa a wannan yankin,inda a daren jiya su ka kutsa cikin unguwanni mabanbanta.
Har ila yau, sojojin mamayar sun kwace gidajen Falasdinawa da dama da suke a kusa da sansanin Tul-kram, da mayar da su zama sansanonin soja.
Ya zuwa yanzu adadin Falasdinawan da ‘yan sahayoniyar su ka tilastawa yin hijira daga sansanonin Tul-Karam da Nuru-Sahmsh, sun kai 10,000.
Ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinawa ta sanar da cewa, adadin mutanen da su ka yi shahada a cikin kwanaki 21 na hare-hare sun kai 11, yayin da wasu gwammai su ka jikkata.
Mazauna yankin kuwa suna cewa, ‘yan sahayoniyar sun killace yankin, sun kuma yanke ruwa da wutar lantarki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
An ruwaito cewa, shirin aikin noman ranin da aka kaddamar a yankin na Lallashi, zai karade hekta 10, wanda kuma sama da kananan manoma 80, za su amfana da shirin kai tsaye.
Bugu da kari, shirin zai taimaka wajen kara samar da girbin amfanin gona mai yawan gaske tare kuma da kara bunkasa tattalin arzikin jihar baki-daya.
Malam Aliyu Musa, da yake yin jawabi a madadin sauran manoman da ke yankin ya bayyana cewa, samar da shirin a yankin da gwamnatin jihar ta yi, tamkar zuba hannun jari ne.
A cewarsa, al’ummar yankin za su ci gaba da yin addu’a, domin shirin ya dore tare kuma da ganin an kara fadada shi, don su ma sauran yankunan jihar su amfana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp