HausaTv:
2025-03-22@13:11:34 GMT

A Kalla Mutane 48 Ne Su Ka Mutu A Wajen Hako Zinariya  A Kasar Mali

Published: 16th, February 2025 GMT

A jiya Asabar ne aka sami hatsari a wani wurin hako zinariya dake yammacin kasar Mali da hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 48.

‘Yan sanda a yankin da lamarin ya faru ne su ka sanar da faruwar hatsarin a wurin da ake hako zinariya ba tare da izinin hukuma ba,wanda kuma ya rutsa da wata mace da karamin yaronta.

Wani jami’in yankin da lamarin ya faru ya bayyana cewa, lamarin ya faru ne a wani wurin hako zinariya da aka kauracewa,da a halin yanzu mata ne su ka fi hako zinariya a cikinsa.

A nashi gefen shugaban hukumar masu hako zinariya a kasar ta Mali Abubakar Keita ya bayyana cewa; A kalla mutane 48 ne su ka kwanta dama sanadiyyar afkuwar wannan hatsarin.

Daga lokaci zuwa lokaci ana samun afkuwar irin wannan hatsarin  a cikin kasashen yammacin Afirka da ake hako zinariya ba bisa izinin mahukunta ba, kuma ba bisa tsari ba.

Mali tana cikin kasashen da suke da wuraren hako ma’adanai mafi girma a cikin yammacin Afirka wanda yake taka rawa a kasafin kudin kasar da kawo ¼.

A watan Disamba na shekarar da ta gabata, ministan kudi na kasar ta Mali Alosini Sano ya ce, kasarsa ta gudanar da wani bincike da sake yin bitar wata yarjejeniya akan cinikin zinariyar da ya ba ta damar dawo da kudaden da sun kai kudin Farank biliyan 700, wato  fiye da Euro biliyan daya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hako zinariya

এছাড়াও পড়ুন:

Dubban Mutane Sun Fito Zanga-Zangar Yin Allawadai Da Kama Magajin Garin Istambul

Dubban dubatan mutane masu goyon bayan magajin garin Istambul a kasar Turkiya ne suka fito kan titunan birnin inda suke bukatar gwamnatin Urdugan ta sake shi.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa mutane suna ganin Ekrem Imamoglu, dan takarar shugaban kasa ne a zaben shugaban kasa mai zuwa kuma mai yuwa ya kara shugaban Urdugan a zaben, saboda yawan magoya bayansa a kasar, musamman a birnin Istambul.

Labarin ya kara da cewa Imamoglu mutum ne wanda yake da karbuwa a cikin mutanen kasar, wanda kuma ana ganin mai yuwa ya kada shugaba Urdugan a zaben shugaban kasa mai zuwa. Don haka ana ganin gwamnatin Urdugan ta sa aka kamashi, tare da zargin cin hanci da rashawa, don bata sunansa.

Gwamnatin Urdugan ta yi amfani da Jami’an tsaro don murkushe zanga-zangar masu goyon bayan magajin garin a jiya Alhamis, saboda ya ci gaba da zama mutumin da aka fi son ya ci gaba da shugabancin kasar.

Banda haka gwamnatin Urdugan ta kama Imamoglu ne bayan koma bayan da jam’iyyarsa ta gamu da shi a wani zaben da aka yi a kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa ta mutu
  • Dubban Mutane Sun Fito Zanga-Zangar Yin Allawadai Da Kama Magajin Garin Istambul
  • Gobara Ta Babbake Wani Shago A Jihar Kwara
  • Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe
  • Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja
  • Mutane Da Dama Ne Ake Jin Tsoron Sun Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Daukar Gas Ta Yi Bindiga A Kan Gadar Karu A Birnin Abuja
  • Nijar, Burkina Faso da Mali sun fice daga kungiyar kasashe renon Faransa
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja