HausaTv:
2025-02-20@08:56:09 GMT

A Kalla Mutane 48 Ne Su Ka Mutu A Wajen Hako Zinariya  A Kasar Mali

Published: 16th, February 2025 GMT

A jiya Asabar ne aka sami hatsari a wani wurin hako zinariya dake yammacin kasar Mali da hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 48.

‘Yan sanda a yankin da lamarin ya faru ne su ka sanar da faruwar hatsarin a wurin da ake hako zinariya ba tare da izinin hukuma ba,wanda kuma ya rutsa da wata mace da karamin yaronta.

Wani jami’in yankin da lamarin ya faru ya bayyana cewa, lamarin ya faru ne a wani wurin hako zinariya da aka kauracewa,da a halin yanzu mata ne su ka fi hako zinariya a cikinsa.

A nashi gefen shugaban hukumar masu hako zinariya a kasar ta Mali Abubakar Keita ya bayyana cewa; A kalla mutane 48 ne su ka kwanta dama sanadiyyar afkuwar wannan hatsarin.

Daga lokaci zuwa lokaci ana samun afkuwar irin wannan hatsarin  a cikin kasashen yammacin Afirka da ake hako zinariya ba bisa izinin mahukunta ba, kuma ba bisa tsari ba.

Mali tana cikin kasashen da suke da wuraren hako ma’adanai mafi girma a cikin yammacin Afirka wanda yake taka rawa a kasafin kudin kasar da kawo ¼.

A watan Disamba na shekarar da ta gabata, ministan kudi na kasar ta Mali Alosini Sano ya ce, kasarsa ta gudanar da wani bincike da sake yin bitar wata yarjejeniya akan cinikin zinariyar da ya ba ta damar dawo da kudaden da sun kai kudin Farank biliyan 700, wato  fiye da Euro biliyan daya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hako zinariya

এছাড়াও পড়ুন:

Turkiya Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Sulhu Tsakanin Habasha Da Somaliya

An yi zaman farko na tattaunawar sulhu a tsakanin kasashen Habasha da Somaliya a birnin Ankara wanda kasar Turkiya take a matsayin mai shiga tsakani.

Ministan harkokin wajen kasar Turkiya Hakan fidan ya yi ganawa da  daban-daban da ministocin harkokin wajen kasashen na Habasha da Somaliya.

Bayan wannan ganawar minstan harkokin wajen na Turkiya ya bayyana cewa; Yin aiki tare a tsakanin kasashen yankin yana da matukar muhimmanci a wannan zamanin da duniya take cike da sarkakiya.” Haka na kuma ya kara da cewa:  Kai wa ga nasara a wannan tattaunawar yana da matukar muhimmanci fiye da kowane lokaci a baya.

Kamfanin dillancin labarun “Anatol” na Turkiya ya nakalto ministan harkokin wajen kasar yana yin ishara da babbar dama da aka samu a wannan lokacin domin ayyana makomar yankin na zirin Afirka, da kuma mayar da kalubalen da ake fuskanta ya zama wata dama

Minista Fidan ya kuma ce, tattaunawar da ake yi ba za ta takaita akan warare sabanin da yake a tsakanin kasashen na Habasha da Somaliya ba, zai zama mai wakiltar mahanga faffada ta siyasar nahiyar Afirka baki daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Turkiya Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Sulhu Tsakanin Habasha Da Somaliya
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa; Yahudawan Sahayoniyya Sun Kasa Murkushe Gwagwarmaya
  • Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Wani Abu A Kasuwar Zamfara
  • Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Ga Tattaunawar Amurka Da Rasha Kan Rikicin Ukraine
  • Gubar harsashi ta jikkata mutane dama a Zamfara
  • Janye Tallafin Amurka Ya Jefa Masu Fama Da Cutar HIV A Kasar Afirka Ta Kudu Cikin Fargaba
  • Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne
  • Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon