Kifi jinsin Shark ya fusata ya fasa rufin gida
Published: 16th, February 2025 GMT
Wani kifi jinsin Shark da mamallakin Kamfanin Airbnb da ya shahara a duniya mai tsawon kafa 25 ya fusata, inda ya fito daga rufin gidan da yake saboda matakin da aka ɗauka na tilasta rufe gidan da aka ajiye shi.
Mamallakin Kamfanin wanda yake mazaunin Birtaniya ne, mai suna Dakta Magnus Hanson-Heine ya rasa wani shirin neman alfarma daga Karamar Hukumar Oxford na hana shi amfani da wurin zama na ɗan gajeren lokaci na cikin kadarorinsa da aka fi sani da Shark House (wato inda yake kiwon kifin).
Ya yi iƙirarin cewa bai samu ƙorafi ko ɗaya daga makwabtansa ba, amma kuma hukumar yankin ta gabatar masa da korafi a kan a rufe gidan AirBnbs da ke cikin birnin.
Haka kuma, a yanzu ya buƙaci baki da su zo, su ziyarci gidan yadda za su iya, inda ya yi alkawarin ci gaba da gudanar da harkoki yadda zai iya.
Mutumin wanda mahaifin HansonHeine da Bill Heine, ya fara gina wannan gidan ba tare da izinin Karamar Hukumar Birnin Oxford a 1986 ba.
A shekaru biyar da suka gabata, ya bayar da hayar kadarorin a karkashin Kamfanin Airbnb na dan gajeren lokaci – amma ya sami sanarwa daga karamar hukumar a kan rufe gidan, bayan wani makwabcin yankin da ya koka game da canjin wurin zama zuwa wani wuri na ɗan gajeren lokaci.
Yanzu an sanar wa Hanson-Heine cewa, dole ne ya daina amfani da gidan na ɗan gajeren lokaci kafin 11 ga Maris, 2025 – matakin da ya yi imanin zai cutar da kamfaninsa dangane da yawon buɗe ido a Oxford gaba ɗaya.
“Gidan Shark babban wurin ɗaukar hankali ne na yawon buɗe ido, ba kawai kamar gidan iyali na yau da kullum ba ne.
“Abin farin ciki ne na sanar da jama’a domin su yi murna tare da mu, kuma zan ci gaba da yin hakan tsawon lokacin da zan iya,” in ji shi.
“Har yanzu ban ji wasu korafe-korafe daga makwabtanmu ba, ko da a lokacin da ake shirin daukaka ƙarar, kuma sufeton yankin bai samu wani nakasu ba a hukuncin da ya yanke,” in ji shi.
Ya ce ya samar da wannan wurin ne don yawon bude ido da yake daukar hankalin baki masu ziyartar wuraren da ya buɗe.
“Wasu daga cikin ’yan majalisar sun yi amfani da wannan a matsayin uzuri don samun wasu hujjoji na siyasa ta hanyar bin taswirar wani yanki na cikin gari don cin gajiyar jama’a,” in ji shi.
“Wannan bai ba da wani abu mai ma’ana ba, don taimaka wa mutanen da ke neman wuraren yawon buɗe ido.
“A bangaren yawon bude ido da masaukin baki yankin Oxford zai kasance mafi muni a gare shi.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Shark
এছাড়াও পড়ুন:
Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
Kasashen Iran da Hadaddiyar Daular Larabawa sun bayyana matukar damuwarsu kan yadda gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta sake dawo da yakin kisan kare dangi a zirin Gaza da kuma hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen.
A wata tattaunawa ta wayar tarho a wannan Juma’a, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da takwaransa na UAE Abdullah bin Zayed Al Nahyan, sun tattauna batutuwan da suka shafi yankin, musamman ma ayyukan wuce gona da iri na Isra’ila a Gaza da kuma hare-haren Amurka a Yemen.
Araghchi ya yi kakkausar suka kan kisan gillar da gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta yi wa daruruwan Falasdinawa da ba su ji ba ba su gani ba tun daga ranar Talata, yana mai jaddada cewa yin hakan saba yarjejeniyar tsagaita bude wuta ne da aka rattaba hannu a kansa.
Ya kuma yi Allah wadai da hare-haren da sojojin Amurka ke ci gaba da kai wa kasar Yemen, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mata da kananan yara da dama, tare da lalata muhimman ababen more rayuwa na yankin, da kuma jefa mutane cikin kangin talauci da yunwa.
Araghchi ya kara da cewa, laifuffukan da gwamnatin yahudawan sahyoniya ke aikatawa a Gaza da kuma harin da Amurka ta kai kan kasar Yaman na bukatar daukar matakin gaggawa da hadin gwiwa daga kasashen yankin da kum akasashen musulmi, domin dakatar da wannan ta’addanci da ke ci gaba da kawo rashin tsaro a duk fadin yankin gabas ta tsakiya.
A nasa bangaren, Ministan kasar UAE Abdullah bin Zayed ya bayyana matukar damuwarsa kan tabarbarewar al’amura a yankin, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin damuwa matuka.
Ya jaddada bukatar ci gaba da tuntubar juna tsakanin kasashen yankin domin hana ci gaba da tabarbarewar zaman lafiya.
Rahotanni sun tabbatar da cewa sojojin Isra’ila sun zafafa kai hare-hare ta sama da kuma ta kasa a zirin Gaza tun daga ranar Talata, inda suke kai hari kan wuraren zaman jama’a da hakan ya hada da wuraren da aka tsugunnar da dubban mutane da suka rasa muhallansu da kuma gidaje, gami da asibitoci, tare da hana duk wasu ayyuka na jin kai ko ceton jama’a ko kai daukin gaggawa.