Aminiya:
2025-03-23@04:00:49 GMT

Gwamnatin Yobe Ta Ɗauki Jami’an Kiwon Lafiya 42 Aiki

Published: 16th, February 2025 GMT

Hukumar kula da lafiya a matakin farko ta Jihar Yobe ta dauki ma’aikatan jinya 42 aiki domin inganta ayyukan kiwon lafiya a jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Adamu Abba ya fitar a Damaturu.

Kifi jinsin Shark ya fusata ya fasa rufin gida Mazabar Tsanyawa/Kunchi ta shafe shekara guda ba tare da wakilci ba

Ya ce tuni babban sakataren hukumar Babagana Machina ya gabatar da wasikun nadin aiki ga ma’aikatan jinya da aka zabo wadanda suka kammala karatun horon su daga kwalejin jinya da ungozoma ta Shehu Sule da ke Damaturu.

Abba ya kara da cewa ma’aikatan jinya za su cike gibin ma’aikata a cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko na kananan hukumomi 17 na jihar.

“Gwamnatin Mai Mala Buni ya zuwa yanzu, ta gyara tare da gina sabbin cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko guda 142 a fadin jihar tun daga shekarar 2019.

“Tun lokacin yakin neman zaben da karo na biyu gwamnan ya yi alkawarin samar da ingantaccen cibiyar kula da lafiya a matakin farko a mazabun 178 da ke Jihar Yobe.

“Saboda haka, wannan daukar ma’aikata da aka yi za su ƙara ƙarfin ma’aikata a cibiyoyin don inganta aikin na kiwon lafiya” in Jin Abba.

Sakataren hukumar, Babagana Machina ya taya ma’aikatan jinya murna yana mai umartar da su mayar da hankali wajen sadaukar da kansu ga ayyukansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Yobe jinya Kiwon Lafiya ma aikatan jinya a matakin farko

এছাড়াও পড়ুন:

Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa

Ƙungiyar Dattawan Arewa (NEF), ta buƙaci Shugaba Bola Tinubu da gaggauta janye dakatarwar da ya yi wa Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin jihar.

Da yake magana a madadin ƙungiyar, Farfesa Abubakar Jika Jiddere, ya ce babu wani dalili da ya dace da zai sa shugaban ƙasa ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar.

Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe

Ya bayyana cewa, kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanadi ayyana dokar ta-ɓaci ne kawai a lokuta na matsanancin rikici kamar yaƙin basasa, ko rushewar doka da oda, wanda a cewarsa babu ɗaya daga cikinsu da ya faru a Jihar Ribas.

NEF, ta zargi Gwamnatin Tarayya da yin hakan ne saboda son rai, ba don amfanin al’umma ba.

Ƙungiyar ta yi zargin cewa rikicin siyasar yana da nasaba da taƙaddamar da ke tsakanin gwamnan da aka dakatar da tsohon gwamnan jihar wanda yanzu ministan Gwamnatin Tarayya ne.

Dattawan sun buƙaci gwamnati da ta dawo da dimokuraɗiyya, adalci, da zaman lafiya a Jihar Ribas.

Haka kuma, sun gargaɗi Gwamnatin Tarayya da kada ta bari irin wannan rikicin siyasa ya tsananta a wasu jihohi kamar Kano, inda ake ci gaba da samun saɓani dangane da masarautar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa
  • An Zabi ‘Yan Kasar Zimbabwe  Kuma Mace Ta Farko A Matsayin Shugabar Shugabar Kwamitin  Wasannin Olympic
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i
  • Tinubu ya ba ni riƙon Ribas don wanzar da zaman lafiya — Ibas
  • Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum
  • Wa Ke Dandana Kudar Matakin Harajin Kwastan Da Gwamnatin Amurka Ta Dauka
  • Gwamnatin Nasarawa Ta Fara Aikin Sabunta Asibitoci 58 Don Inganta Lafiyar Jama’a
  • Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati