Gwamnatin Yobe Ta Ɗauki Jami’an Kiwon Lafiya 42 Aiki
Published: 16th, February 2025 GMT
Hukumar kula da lafiya a matakin farko ta Jihar Yobe ta dauki ma’aikatan jinya 42 aiki domin inganta ayyukan kiwon lafiya a jihar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Adamu Abba ya fitar a Damaturu.
Kifi jinsin Shark ya fusata ya fasa rufin gida Mazabar Tsanyawa/Kunchi ta shafe shekara guda ba tare da wakilci baYa ce tuni babban sakataren hukumar Babagana Machina ya gabatar da wasikun nadin aiki ga ma’aikatan jinya da aka zabo wadanda suka kammala karatun horon su daga kwalejin jinya da ungozoma ta Shehu Sule da ke Damaturu.
Abba ya kara da cewa ma’aikatan jinya za su cike gibin ma’aikata a cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko na kananan hukumomi 17 na jihar.
“Gwamnatin Mai Mala Buni ya zuwa yanzu, ta gyara tare da gina sabbin cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko guda 142 a fadin jihar tun daga shekarar 2019.
“Tun lokacin yakin neman zaben da karo na biyu gwamnan ya yi alkawarin samar da ingantaccen cibiyar kula da lafiya a matakin farko a mazabun 178 da ke Jihar Yobe.
“Saboda haka, wannan daukar ma’aikata da aka yi za su ƙara ƙarfin ma’aikata a cibiyoyin don inganta aikin na kiwon lafiya” in Jin Abba.
Sakataren hukumar, Babagana Machina ya taya ma’aikatan jinya murna yana mai umartar da su mayar da hankali wajen sadaukar da kansu ga ayyukansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Yobe jinya Kiwon Lafiya ma aikatan jinya a matakin farko
এছাড়াও পড়ুন:
Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi
Guguwar ruwan sama ya lalata gidaje da dama a ƙaramar hukumar Shanga ta Jihar Kebbi.
Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris ya jajanta wa al’ummar Garin Kestu da ke unguwar Atuwo a Ƙaramar hukumar Shanga, ya kuma buƙaci iyalan waɗanda abin ya shafa da su ɗauki lamarin a matsayin wata ƙaddara.
Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki a NUPRC — Buba Galadima Matatar Ɗangote ta rage farashin fetur zuwa N865Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labaran gwamnan Ahmed Idris ya fitar.
A cewar sanarwar, gwamnan wanda shugaban Ƙaramar hukumar Shanga, Audu Audu ya wakilta, ya ce ruwan sama mai ƙarfi da ya afku a daren ranar Talata ya lalata gidaje da dukiyoyi na miliyoyin Naira.
Ya kuma tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa, gwamnati za ta bayar da tallafi da suka haɗa da kayayyakin gini.
Gwamnan ya kuma buƙace su da su yi haƙuri, inda ya yi alƙawarin cewa nan ba da daɗewa ba gwamnatin jihar za ta kawo musu ɗauki.