Aminiya:
2025-04-14@18:10:16 GMT

Gwamnatin Zamfara ta haramta taruka siyasa saboda tsaro

Published: 16th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Zamfara ta haramta gudanar da tarukan siyasa a faɗin jihar har sai abin da hali ya yi, domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Wannan mataki ya biyo bayan wasu tashe-tashen hankula masu nasaba da siyasa, inda jam’iyyar adawa ta APC ta koka cewa an kai wasu daga cikin jami’anta hari.

Janar Musa ya fallasa ƙasashen da ke ɗaukar nauyin Boko Haram Kifi jinsin Shark ya fusata ya fasa rufin gida Dalilin Haramta Tarukan Siyasa

Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamnan Jihar Zamfara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Al’amuran Jama’a, Mustafa Jafaru Kaura, ya bayyana cewa an ɗauki mataki ne, sakamakon wata hatsaniya da ta auku a Ƙaramar Hukumar Maru.

Ya ce: “Daga yanzu, an haramta duk wani taro ko gangami da zai iya haddasa tashin hankali, musamman ganin yadda aka rasa rayuka da ƙone dukiya mai yawa a Ƙaramar Hukumar.”

Ya kuma ƙara da cewa wannan dakatarwa ba ta dindindin ba ce, illa dai mataki ne na wucin gadi domin kiyaye zaman lafiya a jihar.

Martanin Jam’iyyar APC

A nata ɓangaren, jam’iyyar APC reshen Zamfara, ta soki matakin, inda ta bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne saboda tsoron ƙarfin jam’iyyar a jihar.

Mai magana da yawun jam’iyyar, Malam Yusuf Idris Gusau, ya ce: “Ai abin mamaki ne a ce an hana tarukan siyasa, domin ba gangamin yaƙin neman zaɓe aka shirya ba.

“Babu wata doka da ta hana tarukan jam’iyyu, don haka gwamnati ba ta da hurumin hana mu gudanar da harkokinmu na siyasa.”

Ya ƙara da cewa APC jam’iyya ce mai rijista a ƙasa, kuma mabiyanta suna bin doka ba tare da haddasa wata fitina ba.

Fargabar Ƙarin Tashin Hankali

Ana dai ganin wannan mataki na gwamnati da martanin APC na iya ƙara dagula lamarin siyasa a jihar.

Masana da masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin akwai buƙatar a samu tattaunawa tsakanin ɓangarorin biyu, tare da shiga tsakani da dattawa da jami’an tsaro domin hana rikicin ya tsananta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: martani Siyasa Taruka Zamfara jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari a Kaduna.

Atiku ya samu rakiyar tsofaffin gwamnoni da suka haɗa da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal da wasu jiga-jigan ’yan siyasa.

An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji

Kamar yadda aka wallafa bidiyon ziyarar a Shafin Atiku na Facebook, an rubuta cewa sun ziyarci Buharin, kuma sun sha dariya.

“A matsayina na Wazirin Adamawa, na tsaya domin gudanar da shagungulan Sallah a Adamawa, inda na wakilci Sarkin Adamawa, Lamiɗo Fombina a wasu shagulgulan.

“Yau kuma na kai ziyarar gaisuwar Sallah ga Muhammadu Buhari wanda ya shugabanci ƙasar a tsakanin 2015 zuwa 2023. Na ji daɗin ziyarar, saboda kamar yadda ya saba, ya yi ta ba mu dariya sai da haƙarƙarina suka yi zafi.” Cewar Atiku.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari