Ƴansanda Sun Kama Saurayin Da Ya Kashe Budurwarsa Ta Facebook A Kwara
Published: 16th, February 2025 GMT
Bayan bincike ta hanyar fasaha, an gano inda wayarta take, wanda hakan ya kai ga kama Abdulrahman Bello. Lokacin da aka kama shi, ya amince da laifin kisan Hafsoh da nufin yin sihirin kudi (oshole/ajoo owo).
A binciken da aka yi a gidansa, an samu:
Wayoyi biyu da takalmin mamaciyar
Hannaye da aka sare daga jikin gawarta roba mai dauke da jininta
Adda, wuka, gatari, da akwatin sihiri
Buhun tsafi da tebur da aka yi amfani da shi wajen aikata kisan
An tura Abdulrahman zuwa sashen binciken manyan laifuka (SCID) Ilorin, domin zurfafa bincike da gurfanar da shi a gaban kotu.
Mai martaba Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, ya bayyana takaici kan wannan ɗanyen aiki, yana mai cewa “abin baƙin ciki ne, kuma yana da ban tsoro”.
Ya buƙaci iyaye su ƙara sa ido kan ‘ya’yansu, tare da kula da irin mutanen da suke mu’amala da su.
কীওয়ার্ড: Ƴansanda
এছাড়াও পড়ুন:
An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato
Shanu 36 sun mutu baya ga wasu 42 da ake zargin an ba su guba guba a kusa da yankin mahaɗar Tafi Gana a Ƙaramar Hukumar Bassa ta Jihar Filato.
Shugaban Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah (MACBAN) a Karamar Hukumar Bassa, Ya’u Idris, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yamma lokacin da shanun ke kiwo a yankin.
Ya’u ya ƙara da cewa an sanya guba ne a cikin gauta, waɗanda aka warwatsa a kewayen wurin kiwon kuma shanun suka ci.
Ya ci gaba da cewa sun kai rahoton lamarin ga dukkan hukumomin tsaro ciki har da Hukumar DSS, da ’yan sanda, ya kuma Babban Kwamandan Rundunar ta kuma din ya ziyarci wurin da abin ya faru.
Wannan lamarin ya faru ne kwanaki biyu kacal bayan wani mummunan hari a kauyen Zikke, a cikin wannan ƙaramar hukumar ta Bassa, inda aka kashe mutane 52 tare da jikkata wasu da dama. An kuma kona gidaje da dama a harin.
Mazauna yankin da aka kai harin sun zargi makiyaya da hannu a kashe-kashen da aka yi a ranar Litinin, zargin da makiyayan suka musanta.
Kakakin rundunar tsaro ta Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, bai amsa saƙon da wakilinmu ya aike masa ba game da lamarin a lokacin da ake rubuta wannan rahoto.
A sakamakon ƙaruwar rashin tsaro, Gwamna Caleb Mutfwang a ranar Laraba ya haramta kiwon dabbobi da daddare, da kuma jigilar shanu da hawa babura bayan ƙarfe 7 na yamma. Wannan matakin na daga cikin hanyoyin da gwamnatin jihar ta ɗauka domin hana ci gaba da samun sabani tsakanin makiyaya da manoma.
Gwamnan, a cikin wani jawabi da ya yi wa al’ummar jihar a ranar Laraba, ya bayyana cewa a makon da ya gabata, an kai hari kauyen Zikke inda aka kashe mutane da dama.
Sai dai, wannan dokar ta haifar da ce-ce-ku-ce, musamman ma daga direbobin manyan motocin da ke Jos, waɗanda suka bayyana haramcin jigilar shanu bayan karfe 7 na yamma a matsayin wanda ya ci karo da wata doka da ta riga ta hana zirga-zirgar manyan motoci tsakanin karfe 6 na safe zuwa 9 na yamma. Sun kuma roƙi gwamnatin da ta sake duba wannan doka.
Haka kuma, kungiyar MACBAN ta nuna damuwarta game da wannan doka, inda ta bayyana cewa lokacin da aka ƙayyade zai iya shafar rayuwar makiyaya, musamman wadanda za su iya kasancewa tare da shanunsu a kasuwanni bayan karfe 7 na yamma.
Sun cewa suna goyon bayan dokar domin tabbatar da zaman lafiya, amma suna roƙo gwamnan da ya ɗaga lokacin zuwa karfe 8 na dare domin mutanensu su samu damar komawa gida lafiya.
Laifin gwamnatocin baya ne — GadgiA nasa ɓangaren, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Pankshin Kanke da Kanam a Jihar Filato, Yusuf Adamu Gagdi, ya bayyana cewa abin takaici ne yadda yankunan da suka yi fice wajen noma a Bokkos, Bassa, Wase, da Mangu suka zama filin daga.
Ya zargi gazawar gwamnatocin baya wajen ba kama shugabannin hukumomin tsaro da laifin gazawarsu wajen samar da tsaro a yankunansu da ta haifar da karuwar matsalar tsaro a kasar.
Gadgi ya kuma alaƙanta ƙaruwar hare-hare a Filato da tserewar da ’yan bindiga ke yi daga jihohi Zamfara da Sakkwato zuwa dajin Filato sakamakon ragargazarsu da sojoji suka tsananta.
Za mu dawo da zaman lafiya — ’yan sandaMataimakin Sufeto Janar na ’Yan Sanda (DIG) Kwazhi Bzigu Dali ya ziyarci yankunan da aka kai hari domin tantance halin da ake ciki, inda ya gudanar da sintiri ta sama da ƙasa tare da ganawa da shugabannin ƙananan hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki.
Ya kuma tabbatar wa mazauna yankin da cewa Sufeto-Janar na ’Yan Sanda ya ƙudiri aniyar dawo da zaman lafiya, inda ya sanar da tura karin jami’an tsaro da kayan aiki.
Dattawan Arewa sun fusataƘungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta yi kakkausar suka ga kashe-kashen da ake yi a Filato, inda ta bayyana su a matsayin abin kunya ga ƙasa.
Sun soki rashin ɗaukar mataki da Gwamnatin Tarayya ke yi, suna masu kira da a tura jami’an tsaro da kayan aiki nan take tare da tabbatar da an yi adalci.
Haka kuma, Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ta nuna baƙin cikinta game da sake ɓarkewar rikicin a Filato, inda ta yi kira ga shugabannin al’umma da na addini da su tallafa wa Gwamna Mutfwang wajen kwantar da hankula da kuma gina zaman lafiya mai ɗorewa.
Gwamnatin Tarayya ta sake nanata ƙudirinta na kawo ƙarshen rashin tsaro a faɗin ƙasar, inda ta bayyana ƙoƙarin da ake yi na ƙarfafa tsaron kasa.
Tsohon ɗan takarar Shugaban Ƙasa na Jam’iyyar Labour, Peter Obi, ya yi kira ga gwamnatin da ta daina magana ta fatar baki kawai, ta ɗauki matakai na zahiri don kare ’yan Najeriya.