Ƴansanda Sun Kama Saurayin Da Ya Kashe Budurwarsa Ta Facebook A Kwara
Published: 16th, February 2025 GMT
Bayan bincike ta hanyar fasaha, an gano inda wayarta take, wanda hakan ya kai ga kama Abdulrahman Bello. Lokacin da aka kama shi, ya amince da laifin kisan Hafsoh da nufin yin sihirin kudi (oshole/ajoo owo).
A binciken da aka yi a gidansa, an samu:
Wayoyi biyu da takalmin mamaciyar
Hannaye da aka sare daga jikin gawarta roba mai dauke da jininta
Adda, wuka, gatari, da akwatin sihiri
Buhun tsafi da tebur da aka yi amfani da shi wajen aikata kisan
An tura Abdulrahman zuwa sashen binciken manyan laifuka (SCID) Ilorin, domin zurfafa bincike da gurfanar da shi a gaban kotu.
Mai martaba Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, ya bayyana takaici kan wannan ɗanyen aiki, yana mai cewa “abin baƙin ciki ne, kuma yana da ban tsoro”.
Ya buƙaci iyaye su ƙara sa ido kan ‘ya’yansu, tare da kula da irin mutanen da suke mu’amala da su.
কীওয়ার্ড: Ƴansanda
এছাড়াও পড়ুন:
An Kashe Askarawa 6 da ‘Yan Sa-kai 4 A Zamfara
Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana alhini tare da yin addu’a ga waɗanda suka rasu, tana fatan samun zaman lafiya mai ɗorewa a jihar da ƙasar baki-ɗaya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp