Ministan Gwamnatin Isra’ila Ya Jaddada Matakin Korar Falasdinawa Daga Zirin Gaza
Published: 16th, February 2025 GMT
Ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya yi furuci da cewa: Nan da wasu ‘yan makonni za a fara tilastawa Falasdinawa mazauna Gaza fara yin gudun hijira
Ministan kudin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Bezalel Smotrich ya bayyana cewa: Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana tuntubar Amurka domin tattaunawa kan aiwatar da shirin shugaban Amurka Donald Trump na tsugunar da mazauna Zirin Gaza a wasu kasashe.
A wata hira da ya yi da tashar talabijin ta 12 ta haramtacciyar kasar Isra’ila Smotrich ya furta cewa: Za a fara aikin kwashe mutanen daga Gaza nan da makonni masu zuwa.
Smotrich ya ci gaba da cewa: Mazauna Gaza ba za su samu abin da suke nema ba a Gaza nan da shekaru goma zuwa goma sha biyar masu zuwa. Ya ci gaba da cewa: Za su mayar da dukkan mazauna Gaza zuwa garin Jabaliya bayan an dawo yaki, kuma Falasdinawa ba za su ga wani abin neman ba har abada.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: haramtacciyar kasar Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Wa Ke Dandana Kudar Matakin Harajin Kwastan Da Gwamnatin Amurka Ta Dauka
Tun lokacin da Donald Trump ya hau mukaminsa na shugaban kasar Amurka a watan Janairu na bana, sau da dama gwamnatinsa ta dauki matakan kakaba harajin kwastan kan abokan cinikinta. A ganinsa, matakan za su tilasta kamfanoni da su maido da tsarin samar da kayayyaki zuwa Amurka, matakin da zai gaggauta bunkasuwar masana’antun kasar. Ko abin ya tafi kamar yadda Trump ya yi tsamani?
Alal hakika, manufofi marasa dorewa da gwamnatin Trump ta dauka na illata amanar Amurka, har ma hakan ya yi ta dakushe kwarin gwiwar masu zuba jari na ketare da na kamfanonin cikin gidan kasar. Babban mizanin wasu muhimman hannayen jarin Amurka ya yi matukar raguwa kwanan baya, abin da ya shaida damuwar masu zuba jari a duniya kan rikicin ciniki da tafiyar hawainiya a bangaren bunkasuwar tattalin arziki. Ban da haka kuma, kamfanonin kasar Amurka da kamfanoni masu jarin waje dake kasar za su iya fuskantar hauhawar kudaden kashewa, da katsewar tsarin samar da kayayyaki da dai sauran kalubaloli. A idanun masu zuba jari, Amurka ba ta zama wuri mai inganci na zuba jari a halin yanzu. Ke nan yaya za a kai ga kare masana’antun cikin gidan kasar?
Mun Yi Watsi Da Ayyana Dokar Ta-Ɓaci Da Tinubu Ya Yi A Ribas – Shugabannin Adawa Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan GombeBaya ga haka, yanzu al’ummar kasar Amurka na fuskantar hauhawar farashin kayayyaki, har ma bisa nazarin da jami’ar Yale ta yi, an ce ko wane iyalin Amurkawa zai biya karin kudi da yawansa ya kai dala 1600 zuwa 2000 a ko wace shekara, sakamakon karin harajin kwastan da gwamnatin kasar ke bugawa a kan kayayyakin da ake shigar da su daga Mexico, da Canada da Sin.
Kamfanonin dake Amurka da al’ummar kasar, su ne suka fi yin asara karkashin manufar da Trump ya dauka, amma abun tambayar shi ne me ya sa ya yi haka? Kuma wa zai ci gajiyar hakan? (Mai zane da rubutu: MINA)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp