Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Muhimmancin Gudanar Da Safarar Teku
Published: 16th, February 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Tsaron ruwa bai kamata ya zama kayan aikin matsin lamba kan kasashen waje ba
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Bai kamata tsaron teku ya zama wani makami na matsin lamba kan kasashen waje ba, sai dai ya zama sakamakon hadin gwiwa tsakanin kasashen yankin.
A cikin jawabin da ya gabatar a wajen bude taron ministocin kasashen tekun Indiya karo na 8 a birnin Muscat na kasar Oman a yau Lahadi, Araqchi ya ce: A yau mun hadu a kasar da aka sani tsawon shekaru aru-aru a matsayin gada da ta hada tsakanin gabas da yamma, kuma tsakanin manyan wayewa da al’ummomi na kusa da na nesa.
Ya kara da cewa: Kasar Oman, mai masaukin bakin al’adu, ba kawai ta kasance a tsawon lokaci tana taka rawa ba ce a fannin tattalin arziki, har ma ta kasance wata alama ce ta taimakekkeniya da tattaunawa da diflomasiyya mai ma’ana a yankin tekun Indiya, wanda a ko da yaushe ke kan gaba wajen ci gaban duniya, mai taka muhimmiyar rawa a makomar tattalin arzikin kasa da kasa.
Ministan harkokin wajen ya kara da cewa: A tsawon tarihi, tekuna sun kasance tamkar kofofin da suke hada tsakanin wayewa, ba iyakokin kasa ba tsawon dubban shekaru, tekun Indiya ba ruwa ne kawai, har ma ya kasance babbar hanyar kasuwanci, musayar al’adu da ci gaban wayewa. Wannan hanya ta hada ‘yan kasuwa daga gabar tekun Indiya zuwa Afirka, daga tsibiran Indonesiya zuwa Tekun Fasha, da kuma daga Iran zuwa Tekun Bahar Maliya. A lokacin da hanyoyin kasa suke da tsawo kuma ba su da aminci, teku ce ta hada kasashe masu tasowa da kuma samar da sabbin damammaki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tekun Indiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO
A nata martani kuwa, Okonjo-Iweala ta ce, karuwar takun saka ta fuskar cinikayya ya haifar da babban kalubale ga tsarin bunkasar cinikayya da tattalin arzikin duniya. Don haka ta jaddada muhimmancin rungumar budadden salo na bin ka’idar cudanyar mabambantan sassa, kana ta jaddada wajibcin warware dukkanin takaddama ta hanyar tattaunawa mai ma’ana karkashin dandalin WTO. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp