HausaTv:
2025-03-23@03:42:18 GMT

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Muhimmancin Gudanar Da Safarar Teku

Published: 16th, February 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Tsaron ruwa bai kamata ya zama kayan aikin matsin lamba kan kasashen waje ba

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Bai kamata tsaron teku ya zama wani makami na matsin lamba kan kasashen waje ba, sai dai ya zama sakamakon hadin gwiwa tsakanin kasashen yankin.

A cikin jawabin da ya gabatar a wajen bude taron ministocin kasashen tekun Indiya karo na 8 a birnin Muscat na kasar Oman a yau Lahadi, Araqchi ya ce: A yau mun hadu a kasar da aka sani tsawon shekaru aru-aru a matsayin gada da ta hada tsakanin gabas da yamma, kuma tsakanin manyan wayewa da al’ummomi na kusa da na nesa.

Ya kara da cewa: Kasar Oman, mai masaukin bakin al’adu, ba kawai ta kasance a tsawon lokaci tana taka rawa ba ce a fannin tattalin arziki, har ma ta kasance wata alama ce ta taimakekkeniya da tattaunawa da diflomasiyya mai ma’ana a yankin tekun Indiya, wanda a ko da yaushe ke kan gaba wajen ci gaban duniya, mai taka muhimmiyar rawa a makomar tattalin arzikin kasa da kasa.    

Ministan harkokin wajen ya kara da cewa: A tsawon tarihi, tekuna sun kasance tamkar kofofin da suke hada tsakanin wayewa, ba iyakokin kasa ba tsawon dubban shekaru, tekun Indiya ba ruwa ne kawai, har ma ya kasance babbar hanyar kasuwanci, musayar al’adu da ci gaban wayewa. Wannan hanya ta hada ‘yan kasuwa daga gabar tekun Indiya zuwa Afirka, daga tsibiran Indonesiya zuwa Tekun Fasha, da kuma daga Iran zuwa Tekun Bahar Maliya. A lokacin da hanyoyin kasa suke da tsawo kuma ba su da aminci, teku ce ta hada kasashe masu tasowa da kuma samar da sabbin damammaki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: tekun Indiya

এছাড়াও পড়ুন:

Dokar Ta-Ɓaci: Tinubu Ya Kauce Hanya, Ya Ci Zarafin Dimokuraɗiyya A Ribas – Sambauna

A shekarar 2004, lokacin da Olusegun Obasanjo ya ayyana dokar ta-ɓaci a Filato, matakin ya fuskanci suka daga jama’a da ɓangaren shari’a.

Masana doka da ‘yan siyasa sun yi Allah-wadai da matakin da Tinubu ya ɗauka, inda Dokta Reuben Abati ya bayyana shi a matsayin “laifi da za a iya tuhumar Tinubu a kai”.

Ya ce Shugaban Ƙasa ba shi da ikon rushe zaɓaɓɓun shugabanni na jiha.

Bugu da ƙari, Sambauna ya caccaki yadda Gwamnatin Tinubu ke nuna bambanci wajen raba wa matasa tallafi.

Ya ce: “Seyi Tinubu ya bayar da kayan abinci a Arewa a matsayin tallafi, amma a Kudu yana bayar da tallafin kuɗi domin mutane su dogara da kansu wajen bunƙasa kasuwanci. Wannan nuna bambanci ne da bai dace ba.”

Amma, ya buƙaci gwamnati da ta girmama doka da ƙa’idojin dimokuraɗiyya, inda ya ce wannan mataki na Tinubu babbar barazana ce ga mulkin dimokuraɗiyya a Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
  • Gwamnati Ta Jaddada ƙudirin Kare ‘Yancin Faɗin Albarkacin Baki Da ‘Yancin ‘Yan Jarida
  • An Bukaci Gwamnati A Kowani Mataki Da Ta Taimakawa Yaki Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Araghchi : Iran za ta mayar da amsa ga wasikar Trump cikin kwanaki masu zuwa
  • Dokar Ta-Ɓaci: Tinubu Ya Kauce Hanya, Ya Ci Zarafin Dimokuraɗiyya A Ribas – Sambauna
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu
  • Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe