Shirin Inganta Muhalli da Samar da Ruwan sha da kuma bunkasa aikin gona ACRESAL a jihar Jigawa yace zai zabo garuruwa masu wahalar shiga guda 6 domin sanya musu fitilun kan titi masu amfani da hasken rana.

Shugaban shirin na jihar Jigawa, Alhaji Yahaya Muhamamad Uba Kafin Gana ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse, babban birnin Jihar.

Yana mai cewar, a yanzu haka ma tuni an zabi karin wasu garuruwa 60 domin basu bashin kudi marar ruwa.

A don haka, ya bukaci wadanda aka baiwa bashin a baya da su tabbatar sun biya domin wasu su amfana.

Alhaji Muhammad Uba yace Gwamna Umar Namadi ya amincewa shirin ACRESAL sayo karin injinan yashe kogi guda 2, wadanda za a rika amfani da su wajen yashe kogin Hadejia, domin samun saukin sarrafa ruwan kogi don hana ruwa shiga gonaki.

A cewarsa, ACRESAL da ma’aikatar kare muhalli ta jihar za su reni dashen itatuwa miliyan biyar da dubu dari biyar a bana, domin yaki da zaizayar kasa.

Shugaban shjirin na ACRESAL ya kara da cewar a yanzu haka ACRESAL tana gudanar da biyan diyyar naira miliyan 187 ga wadanda aikin zaizayar kasa ya shafi kadarorinsu a unguwannin Dan Masara da kuma Kalgo dake karamar hukumar Dutse.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

IRGC: Za Mu Kai Farmakin “ Wa’adus-Sadik” Na 3 Akan ‘Yan Mamaya

Mataimakin kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran “IRGC” ya sanar da cewa; Iran za ta kai farmakin “Wa’adus-Sadik 3”  a lokacin da ya dace.

Laftanar janar Ali Fadwi ya kuma yi ishara da yakin Gaza, yana bayyana cewa, su kansu ‘yan sahayoniya sun bayyana cewa Hamas ta yi nasara, su kuma ba su cimma manufarsu ba.

Iran dai ta kai wa HKI hare-hare guda biyu a aka bai wa Sunan                    “ Wa’adussadik” na daya da na biyu. Hare-haren na Iran dai sun kasance mayar da martani ne akan harin da HKI ta kai wa  karamin ofishin jakadancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a kasar Syria da kuma kashe mata jami’an soja masu bayar da shawara ga gwamnatin Damascuss. Na biyun kuwa ya kasance mayar da martani akan kisan gillar da ‘yan sahayoniyar su ka kawo a Tehran wanda ya yi sanadiyyar shahadar shugaban kungiyar Hamas Shahid Isma’ila Haniyyah.

A wani gefen, shugaban kungiyar Hamas a yankin Gaza, Khalil Hayyah ya fada a makon da ya shude cewa; Iran ta kasance a sahun gaba wajen taimakawa gwgawarmayar Falasdinu, kuma muna da tabbacin cewa za ta cigaba da yin hakan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • NAJERIYA A YAU: Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano
  • Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi
  • Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.
  • UNICEF Ya Bukaci Hadin Kai Don Inganta Rayuwar Kananan Yara A Jigawa
  • Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwo
  • Gwamnatin Kano Ta Amince Da Biyan Bashin Albashin Ma’aikatan Tsaftar Muhalli 2,369
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa Jihar Jigawa Kayayyakin Noma Na Sama Da Naira Biliyan 5
  • IRGC: Za Mu Kai Farmakin “ Wa’adus-Sadik” Na 3 Akan ‘Yan Mamaya
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Tituna Akan Kudi Naira Biliyan 6.3