Leadership News Hausa:
2025-02-20@09:09:21 GMT

Adadin Kuskuren Da VAR Take Tafkawa Ya Ragu A Wannan Kakar

Published: 16th, February 2025 GMT

Adadin Kuskuren Da VAR Take Tafkawa Ya Ragu A Wannan Kakar

Masu lura da gasar sun ce kwarewar na’urar wajen yanke hukunci ya karu zuwa kashi 96.4 idan aka kwatanta da kashi 95.7% a kakar da ta gabata.

“Babu wanda yake shakku kan tasirin da ko da kuskure daya wajen yanke hukunci zai yi,” in ji wani babban jami’in kwallon kafa, Tony Scholes.

Ya ci gaba da cewa “Mun san cewa kuskure daya tal zai iya cutar da kungiya.

Sakamako da kuma makin da kungiya ke samu na iya sanyawa a kori mai horarwa ko kuma dan wasa ya rasa damarsa a cikin kungiya.”Hakan ya faru ga Erin ten Hag – domin daya daga cikin kurakurai hudu da na’urar VAR ta tafka shi ne bai wa West Ham bugun fanareti a wasa na karshe da kocin ya jagoranci kungiyar Manchester United.

Haka nan wasu alkalan wasan sun fuskanci cin zarafi, inda a kwanakin nan ‘yansanda suka kaddamar da bincike kan “barazanar cin zarafi” kan alkalin wasa Michael Oliber bayan wasan da Arsenal ta yi nasara kan Wolbes da ci 1-0 a watan Janairu. Kuma wannan ya biyo bayan matakin da alkalin wasan ya dauka na bai wa dan wasan Arsenal, Myles Lewsi-Skelly katin kora – matakin da daga baya aka soke bayan korafin da kungiyar ta shigar.

Shi ma tsohon alkalin wasa Dabid Conte, an kore shi ne a watan Disamba bayan binciken da aka gudanar a kansa. Hukumomin gasar Premier dai ba su bayyana lokuta 9 da na’urar VAR ta ki soke wani mataki ba – kuma babu tabbas ko batun jan katin da aka bai wa Lewis-Skelly na ciki amma hukumar ta yi bayani kan kurakurai hudu da na’urar ta tafka ga manema labarai.

Kuskure hudu da VAR ta tafka

Outtara ya ‘taba kwallo da hannu’ – Bournemouth 1-1 Newcastle, 25 ga Agusta.

Abin da ya faru: Dango Outtara ya zaci cewa ya ci wa kungiyarsa Bournemouth kwallon da za ta ba ta nasara lokacin da ya zura kwallon da kai. Lafari Dabid Coote ya bayar da kwallon.

Matakin VAR: Mai kula da na’urar VAR a wasan, Tim Robinson ya bai wa Coote shawarar soke kwallon, inda ya ce an taba kwallon da hannu. Kasancewar yana da yakini kan hukuncinsa, bai bukaci lafari ya kalli bidiyon lamarin ba.

Sakamako: Kasancewar babu cikakkiyar hujjar da za ta tabbatar da cewa kwallon tabbas ta taba hannun Ouattara, shugaban hukumar lura da alkalan wasan gasar Premier, Howard Webb a lokacin da ya tattauna da kafar yada labarai ta Sky Sports, ya ce – VAR ta yi kuskure wajen soke cin kwallon.

 

De Ligt ya kwashe Ings – West Ham 2-1 Man Utd, 27 ga Oktoba

Abin da ya faru: Xan wasan gaba na West Ham, Danny Ings ya fadi a cikin yadi na 18 lokacin da yake fafutikar buga kwallo tsakaninsa da mai tsaron baya na Manchester United, Mathijs de Ligt. Lafari Dabid Coote ya bayar da damar a ci gaba da wasa amma sai mai kula da na’urar VAR, Michael Oliber ya bukaci a sake dubawa a talabijin na gefen fagen wasa.

Matakin VAR: Daga nan ne Coote ya bayar da bugun fanareti, wanda dan wasa Jarrod Bowen ya zura a raga, kuma hakan ya bai wa West Ham nasara a wasan.

Sakamako: Washegari United ta sallami Ten Hag daga aiki. Daga baya Web ya ce bai kamata a bayar da fanaretin ba.

 

Jan katin da aka bai wa Norgaard – Brentford 0-0 Eberton, 23 ga Nuwamba

Abin da ya faru: Xan wasan Brentford, Christian Norgaard ya tokari mai tsaron ragar Eberton, Jordan Pickford a gwiwa lokacin da suke fafutikar kaiwa ga kwallo a cikin yadi na 18.

Mataki VAR: Alkalin wasa Chris Kabanagh bai ce an yi keta ba amma sai mai kula da na’urar VAR ya bukace shi ya sake duba wurin a talabijin din gefen fage. Bayan sake dubawa, nan take ya daga wa Norgaard jan kati.

Sakamako: Kwamiti mai zaman kansa ya soke dakatarwar da aka yi wa Norgard na wasa uku bayan korafi da kungiyar ta Brentford ta shigar.

Soke kwallon da Milenkobic ya zura – Nottingham Forest 3-2 Southampton, 19 ga Janairu.

Abin da ya faru: Nikola Milenkobic ya jefa kwallo a raga da kai inda hakan ya sanya Nottingham Forest ta yi gaba da ci 4-1.

Matakin VAR: Na’urar VAR ta umarci lafari Anthony Taylor ya soke cin saboda dan wasan Forest, Chris Wood ya yi satar fage inda hakan ya hana masu tsaron baya na

Southampton damar kalubalantar kwallon. Wood bai taba kwallon ba.

Sakamako: Kwamiti mai zaman kansa da ya duba lamarin ya ce ya kamata a bayar da cin.

Shin Ko Barcelona Ce Matsalar Dembele?

Tauraruwar dan wasa Ousmane Dembele tana ci gaba da haskawa tun bayan barinsa kungiuar kwallon kafa ta Barcelona inda ya ci gaba da saka kwazo a cin kwallaye, bayan da Paris St-Germain ta je har gida ta doke Brest 3-0 a wasan cike gurbi a Champions League ranar Talata inda Dembele ya zura kwallo biyu a raga karo na 10 yana cin kwallaye a jere a PSG, kuma na 18 jimilla a wasa 11 baya a dukkan fafatawa.

Xan wasan tawagar Faransa ya ci uku rigis a gasar zakarun Turai da Stuttgart kuma a tarihi wasu ‘‘yan wasa kadan ne da suka zura kwallo uku rigis a wasa biyu a jere a Champions League da ya hada da Lionel Messi a Barcelona a 2016 da Cristiano Ronaldo a Real Madrid a 2017.

Dembele bai samu kafa wannan tarihin ba, wanda aka sauya shi da Goncalo Ramos a minti na 82 a fafatawar. Kenan Dembele ya ci kwallo 14 a Ligue 1 da Champions League a 2025.

Tun kafin Dembele ya zura biyu a ragar Brest, Vitinha ne ya fara ci a bugun fenariti a minti na 21 da fara wasan kuma wannan shi ne wasan farko zagayen cike gurbi a sabon fasalin Champions League, za su kara a wasa na biyu a Paris ranar 19 ga watan Fabrairu. PSG, wadda ba ta taba daukar Champions League ba, an kusan fitar da ita a gasar bana a cikin rukuni, daga baya ta kara kwazo da ta doke Manchester City da Stuttgart a wasanninta na gaba.

Ana sa ran PSG za ta kai zagayen gaba cikin ruwan sanyi, wadda ake sa ran watakila ta fuskanci Liberpool ko kuma Barcelona a zagayen ‘yan 16.

 

 

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Var

এছাড়াও পড়ুন:

Ukraine ce mai laifi a yaƙin da ta ke yi da Rasha — Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya soki shugabancin Ukraine, inda ya bayyana cewar su ne suka haddasa yaƙin da Rasha ke yi da su.

Trump, ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani ga shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, wanda ya ce yana mamakin yadda ba a gayyaci ƙasarsa zuwa taron tattaunawar zaman lafiya a Saudiyya ba.

’Yan bindiga sun kashe mutum 2, sun sace manoma 10 a Neja ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa

A cewar Trump, Ukraine ce ta jawo wa kanta matsalar.

“Da ba ku fara wannan yaƙin ba, da kun cimma yarjejeniya tun farko,” in ji shi.

“Da ni ne, da na samo muku mafita, kuma babu wanda za a kashe.”

A Saudiyya, Rasha da Amurka sun fara tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin.

Ministan harkokin wajen Rasha, Sergei Lavrov, ya ce: “Ba za mu amince da dakarun Nato a Ukraine ba.”

Lavrov ya ce Rasha na son tattaunawa, amma ba za ta yarda da wata yarjejeniya da za ta bai wa Nato damar girke dakarunta a Ukraine ba.

A nasa ɓangaren, Zelensky ya mayar da martani da cewa Rasha ba abin dogaro ba ce.

“Rasha ba abin yarda ba ce. Dole ne a tilasta mata zaman lafiya.”

Trump ya kuma soki Ukraine kan rashin gudanar da zaɓe tun bayan fara yaƙin.

“Shin ’yan Ukraine ba za su iya fita su zaɓi shugabansu ba? An ɗauki tsawon lokaci ba a yi zaɓe ba.”

Ya ƙara da cewa Ukraine ta rasa goyon bayan jama’arta, yana mai iƙirarin cewa Zelensky ya rasa kashi huɗu cikin 10 na magoya bayansa.

A yayin da ake ci gaba da rikici, Amurka da ƙasashen Turai na ƙoƙarin samun mafita, amma Trump ya ce Amurka ba za ta tura dakarunta zuwa Ukraine ba.

“Idan Turawa suna son yin yaƙi, abu ne mai kyau, ina goyon baya,” in ji Trump.

“Amma Amurka ba ta da nasaba da wannan rikici.”

Taron Saudiyya dai na ɗaya daga cikin matakan tattaunawa tsakanin manyan ƙasashen don kawo ƙarshen wannan rikici, wanda ya haddasa asarar rayuka tun a shekarar 2022.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Ce Tana Iya Sakin Dukkan Fursinonin Yahudawa Gaba Daya A Lokaci Guda
  • Real Madrid ta fitar da Man City a Gasar Zakarun Turai
  • UCL: Real Madrid ta murƙushe Man City da ci 3
  • Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi
  • Ukraine ce mai laifi a yaƙin da ta ke yi da Rasha — Trump
  • An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kungiyar Manyan Sakatarorin Jihar Zamfara
  • Yadda Fim Din “Ne Zha 2” Ya Samu Matukar Karbuwa A Duniya Bai Zo Da Mamaki Ba
  • Da wahala City ta yi nasara a gidan Madrid — Guardiola
  • Yawan Tikitin Kallon Fim Din “Ne Zha 2” Da Aka Sayar a Karshen Mako Ya Shiga Sahun Gaba Na Fina-Finai 5 A Arewacin Amurka
  • FG Ta Jaddada Bukatar Samarda Sabbin Ka’idojin Visa Domin Taimakawa Kasuwancin A Duniya