Jaridar kimiyya da fasaha ta kasar Sin ta ba da rahoton cewa, kwamfutar da kasar Sin ta kera da kanta ta zamani na uku mai sarrafa bayanai tare da warware matsaloli cikin matukar sauri ko kwamfutar quantum a takaice, wato Origin Wukong, ta samu masu amfani da ita sama da miliyan 20 daga sassan duniya baki daya, wanda ya kasance wani muhimmin ci gaba a fannin bunkasa ayyukan da suka shafi kwamfutar quantum.

A cewar cibiyar nazarin injiniyan kwamfutar quantum ta Anhui, masu amfani daga kasashe ko yankuna 139 sun samu damar shiga Origin Wukong, tare da Amurka, Rasha, Japan da Kanada a matsayin mafi yawan yin amfani da ita. A cikin wadannan kasashe, Amurka ce ke kan gaba a ziyarar masu amfani daga kasashen waje. (Mohammed Yahaya)

 

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv

Dakarun Falasdinawa sun mayar da martani ga kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa fararen hula bayan sake dawo da yakin Isra’ila a kan al’ummar Gaza, inda suka harba rokoki zuwa Tel Aviv.

Al-Qassam Brigades, reshen soji na kungiyar gwagwarmayar Islama ta Hamas, ta sanar a wannan  Alhamis cewa, ta yi ruwan makamai masu linzami samfurin M90 a kan birnin Tel Aviv, a matsayin mayar da martani ga kisan kiyashi da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi kan fararen hula a zirin Gaza.

Sojojin mamaya na Isra’ila sun tabbatar da cewa sun gano wasu rokoki guda uku da aka harba daga Gaza zuwa tsakiyar Falasdinu da suka mamaye, tare da jin karar makamai a sararin samniyar Tel Aviv, Gush Dan, da matsugunan yahudawa da ke kewaye.

Isra’ila bat a mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta ba, kamar yadda ta yi fatali da mataki na biyu na yarjejeniyar , tare da sanya wasu sharudda da gangan domin matsin lamba a kan kungiyoyin  gwagwarmayar Falasdinu.

Isra’ila Ta sake sabunta kai hare-hare a zirin Gaza, inda ta kai hari a wurare daban-daban na yankin tun daga kwanaki biyu zuwa uku da suka gabata har zuwa yau.

Hare-haren na Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun yi sanadin shahadar daruruwan fararen hula, galibi mata da kanan yara, tare da jikkata wasu da dama .

Wakilin Al-Mayadeen ya tabbatar da cewa sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila sun sake raba arewacin Gaza daga tsakiya da kuma kudancin yankin, inda suka sake kwace iko da yankin Netzarim.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa
  •  “Yan Ta’adda Sun Kai Hari Akan Masu Salla A Jamhuriyar Nijar
  • An Zabi ‘Yan Kasar Zimbabwe  Kuma Mace Ta Farko A Matsayin Shugabar Shugabar Kwamitin  Wasannin Olympic
  • Manufofin Kasar Sin Sun Zamo Jagora Ga Duniya A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama
  • Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe
  • ‘Za a fara biyan Naira 77,000 ga masu yi wa ƙasa hidima daga Maris’
  • Wa Ke Dandana Kudar Matakin Harajin Kwastan Da Gwamnatin Amurka Ta Dauka
  • Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv
  • Sojojin Yamen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI
  • A Jiya Laraba Ce Iran Take Bukukuwan Cika Shekaru 78 Da Kwatar Kamfanin Man Fetur Na Kasar Daga Hannun Turawan Burtaniya