Leadership News Hausa:
2025-03-23@09:51:53 GMT

Yadda Ake Magance Kumburin Idanu?

Published: 16th, February 2025 GMT

Yadda Ake Magance Kumburin Idanu?

Shan ruwa hanya ce mafi sauwi wajen magance kumburin ido domin, ruwa yana wanke dauda a Ido. A samu cokulan karfe kamar biyar zuwa shida a saka a firiji na tsawon minti 10 zuwa 15 sannan a cire su, sai a rika shafawa a kumburin Ido har sai ido ya sabe.

Ganyen shayi yana magance kumburin Ido: A jika ganyen shayi a ruwan dumi, sannan a cire a bari ya huce.

Sai a kwanta a dora jikakkiyar jakar ganyen shayin a kan idanu sai a rufe idanu da kyalle mai tsabta.

A bari ya tsaya a hakan na tsawon minti biyar zuwa goma sannan a cire.

Wata hanyar magance kumburin ido ita ce: A samu gurji a yanka sannan a saka a firiji na tsawon minti goma sai a cire a dora a kan Idanuwan har sai sun huce.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An wawushe motar abinci ta Hukumar WFP a Borno

Wasu da ba a san ko su wanene ba sun yi awan gaba da kayayyakin wata mota ɗauke da kayan abinci na Hukumar abinci ta duniya (WFP) a garin Gubio, yayin da take kan hanyarta ta zuwa Damasak a Jihar Borno.

Majiyar leƙen asiri ta shaidawa Zagazola Makama cewa, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:30 na rana lokacin da Aminu Malam Umar direban wata babbar mota ƙirar Iɓeco ya tsaya a gefen titi.

’Yan adawa sun shirya ƙalubalantar Tinubu a zaɓen 2027 – Atiku Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe

Yayin da motar ta tsaya a gefen titi ba tare da kula daga jami’an tsaro ba, wasu da ba a san ko su waye ba suka sace buhunan shinkafa da gishiri da sukari da wake da kuma man girki da dama, duk da cewa ba a tantance adadin da kuma darajar kayayyakin da aka sace ba har ya zuwa yanzu.

Jami’an tsaro sun ziyarci wurin da lamarin ya faru, amma ba a kama kowa ba.

Daga bisani sojoji sun ɗauke motar zuwa  Gubio lafiya lau a yayin da ake ci gaba da bincike don gano waɗanda suka aikata laifin tare da ƙwato kayayyakin da aka sace.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ake noman gurjiya
  • Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027
  • Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban
  • An Rantsar Da Sabuwar Shugabar Kasar Namibia
  • Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia
  •  HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
  • Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban Miyetti Allah A Filato
  • An wawushe motar abinci ta Hukumar WFP a Borno
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu