Leadership News Hausa:
2025-04-14@18:14:57 GMT

Yadda Ake Magance Kumburin Idanu?

Published: 16th, February 2025 GMT

Yadda Ake Magance Kumburin Idanu?

Shan ruwa hanya ce mafi sauwi wajen magance kumburin ido domin, ruwa yana wanke dauda a Ido. A samu cokulan karfe kamar biyar zuwa shida a saka a firiji na tsawon minti 10 zuwa 15 sannan a cire su, sai a rika shafawa a kumburin Ido har sai ido ya sabe.

Ganyen shayi yana magance kumburin Ido: A jika ganyen shayi a ruwan dumi, sannan a cire a bari ya huce.

Sai a kwanta a dora jikakkiyar jakar ganyen shayin a kan idanu sai a rufe idanu da kyalle mai tsabta.

A bari ya tsaya a hakan na tsawon minti biyar zuwa goma sannan a cire.

Wata hanyar magance kumburin ido ita ce: A samu gurji a yanka sannan a saka a firiji na tsawon minti goma sai a cire a dora a kan Idanuwan har sai sun huce.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran babban titin Abuja-Kaduna-Zariya-Kano, wadda ke da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin Arewacin Najeriya.

Da yake jawabi a taron kaddamarwar a Kagarko, Jihar Kaduna, Gwamna Uba Sani, ya bayyana yadda aka yi watsi da hanyar da kuma irin mummunan tasirin da hakan ya yi ga rayuka da ci-gaban tattalin arziki.

Gwamna Uba Sani, ya yaba wa Tinubu bisa farfado da aikin, yana mai nuni da muhimmancin hanyar a matsayinta na mafi yawan zirga-zirgar ababen hawa a Arewa.

Da yake ba da tabbacin kamma aikin a cikin watanni 14, Tinubu wanda Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, ya ce za a gina titin ne da kankare, kamar babbar hanyar Legas zuwa Kalaba.

An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu

Ministan ya kara da cewa aikin zan dangana har zuwa filin jirgin sama na Kano, kuma za a sanya kyamarorin CCTV gaba daya a tsawon titin, wanda sabon dan kwangila ne zai aiwatar.

Ya ce, shugaban kasa ya amince da naira biliyan 252 don muhimman sassan aikin, inda aka riga aka biya kashi 30%, yanan mai yaba muhimmiyar rawar da Gwamna Uba Sani ya taka a aikin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  • Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
  • Yadda Ake Tuwan Amala Da Miyar Uwaidu
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)
  • Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (1)
  • Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari