Al’ummar Gundumar Kano Ta Arewa Sun Dara Bayan Kwashe Shekaru 10 Ba Ruwan Sha
Published: 17th, February 2025 GMT
An samar da ruwan sha a yankunan Danbatta, da Makoda da Minjibir dake gundumar Kano ta Arewa bayan kwashe kimanin shekaru goma.
Kwamishinan albarkatun ruwa na jihar Alhaji Umar Haruna Doguwa ya bayyana haka a wani rangadin da ya kai kananan hukumomin uku domin tantance yadda ake samar da ruwan sha ga al’umma.
Umar Doguwa ya bayyana cewa gwamna Abba Kabir Yusuf ya himmatu sosai wajen samar da ruwan sha a dukkan lungu da sako na jihar Kano.
Ya ce an gyara kananan cibiyoyin samar da ruwan sha a yankunan inda ake samar da ruwa babu kakkautawa.
Kwamishinan ya ce yanzu haka ana samun ruwan sha a kauyukan kunya, da Kilawa da ,wailare duk a karamar hukumar Minjibir yayin da ake kokarin ganin an samar da ruwan sha na karamar hukumar Danbatta.
“Abin takaici ne matuka, duk wadannan kauyukan sun shafe sama da shekaru takwas babu ruwa, duk da cewa suna da cibiyoyin samar da ruwan“.
Ya ce a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike a wadannan kauyukan domin tabbatar da cewa an gyara dukkan bututun da a halin yanzu wasu sun yi tsatsa da sauran matsaloli sakamakon rashin amfani da su na tsawon shekaru.
Doguwa ya kara da cewa, hakan na nuni da kokarin gwamna Abba Kabir Yusuf na farfado da samar da tsaftataccen ruwan sha ga al’ummar jihar.
Umar Haruna Doguwa ya ci gaba da cewa gwamnati ba za ta ragawa duk wanda aka samu yana karkatar da ruwan da aka tanadar don sha da amfanin gida ba zuwa gonaki don noman rani.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ruwan Sha samar da ruwan sha ruwan sha a
এছাড়াও পড়ুন:
AU Ta Zabi Sabbin Shugabanni Ana Tsaka Da Tashe-tashen Hankula A Nahiyar
A ranar Asabar din da ta gabata ne shugabannin kasashen kungiyar Tarayyar Afirka AU, suka zabi shugaban kasar Angola Joao Lourenco, a matsayin sabon shugaban karba-karba na kungiyar da kuma ministan harkokin waje da hadin gwiwar kasa da kasa na Djibouti, Mahamoud Ali Youssouf, a matsayin sabon shugaban hukumar gudanar da ayyukan kungiyar, wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun tashe-tashen hankula a kasashe biyu masu matukar muhimmanci a nahiyar, wato Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo (DRC) da kasar Sudan. Rikicin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo na kara kamari, bayan samun galaba a wasu yankunan kasar da ‘yan tawayen M23 suka yi, na baya-bayan nan shi ne kwace iko da muhimman wurare da dama a birnin Bukavu, hedkwatar lardin Kivu ta kudu, da safiyar ranar Asabar, ciki har da gidan gwamnan lardin, makonni biyu bayan kwace babban birnin Goma. DRC dai ta zargi kasar Rwanda da marawa ‘yan tawayen baya, amma Rwanda ta musanta wannan zargin. Tun daga wannan lokacin kawo yanzu, shugabannin nahiyar ba su daina yin kiraye-kiraye da a tsagaita wuta ba tare da wani sharadi ba, da dakatar da tashin hankali da kuma bude manyan hanyoyin samar da kayayyaki da filin jirgin Goma ba. Hakazalika, Sudan ita ma ta kasance wata babban jigon tashe-tashen hankula da shugabannin nahiyar ke tattaunawa. Tsananin wadannan rikice-rikice na iya haifar da yakin yanki, ganin cewa sojojin kasashe makwabta, kamar Afirka ta Kudu sun riga sun shiga kasar Congo Kinshasa. Idan ba mu manta ba, tun bayan manyan yake-yake guda biyu wadanda suka faru tsakanin 1996 zuwa 2003, wanda ya hada da kasashe kusan goma na Afirka, ake zaman dar-dar a gabashin Congo Kinshasa, wanda kuma ke barazanar sake haifar da rikicin kabilanci da na siyasa a yankin manyan tabkuna.
Kungiyoyin kasa da kasa da masu ruwa da tsaki sun yi gargadin cewa idan ba a yi taka tsantsan ba, wannan rikici na iya rikidewa zuwa yakin yanki, sun nakalto bakar azabar da aka fuskanta a tashe-tashen hankulan shekarun 1990. Hakazalika, al’ummar kasa da kasa na fatan sabon shugabancin AU zai dauki kwararan matakai da inganta hadin gwiwa, don kwantar da hankula, da samar da kyakkyawan martani ga duk wani rikicin da ke addabar nahiyar.