Najeriya Ta Ki Amincewa Da Sake Fasalin Siyasa Da Tsaro Na Kungiyar AU
Published: 17th, February 2025 GMT
Najeriya ta nuna adawa da wani yunkuri na sake fasalin Sashen Harkokin Siyasa, Zaman Lafiya da Tsaro na Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) (PAPS), saboda damuwa game sanadin da ka iya tabarbarewar hanyoyin zaman lafiya da siyasa na kungiyar.
Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Tuggar ne ya sanar da wannan matsayi a madadin Shugaba Bola Tinubu, a lokacin da ake tattaunawa kan ssauye-sauyen kungiyar AU.
Shugaban na Najeriya ya kuma yabawa shugabanin kasashen Ruwanda Paul Kagame da William Ruto na Kenya, bisa shawarwarin da suka gabatar na kawo sauyi da nufin ganin kungiyar ta AU ta kara zage damtse wajen magance matsalolin mambobin kungiyar.
Shugaba Tinubu ya bayyana goyon bayansa na samar da kwamitin sa ido kan shugabannin kasa da na gwamnati, wanda shugaba Ruto zai jagoranta, domin sa ido kan sauye-sauyen kungiyar ta AU.
Bugu da kari, ya amince da kudirin takaita ajandar taron kolin kungiyar AU zuwa wasu muhimman abubuwa uku.
Sai dai Tinubu ya ki amincewa da kudirin raba sashen na PAPS, wanda a halin yanzu jami’in diflomasiyyar Najeriya Ambasada Bankole Adeoye ke jagoranta, wanda a kwanan nan aka sake zabensa a karo na 2.
Tinubu ya bayar da hujjar cewa shirin sake fasalin zai haifar da kashe kudade na babu-gaira-babu dalili, da kuma kawo cikas ga wasu ayyukan da aka sa a gaba.
A yayin da yake jaddada gaskiya da kuma hada kai, Tinubu ya yi kira da a dauki matakin yin garambawul ga manufofin kungiyar tarayyar kasashen Afirka wato AU. “Ya kamata mu maida hankali ne kan wuraren da aka riga aka cimma matsaya, maimakon kokarin kara tunkarar wasu sabbin abubuwa.” In ji shi.
Najeriya ta yi alkawarin ci gaba da bayar da goyon baya ga sauye-sauyen kungiyar ta AU ba tare da bata wani lokaci ba, muddin dai sun kasance bisa gaskiya.
Daga Bello Wakili
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: kungiyar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje
Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa babu wata gamayyar ’yan adawa da za ta iya hana Shugaba Bola Ahmed Tinubu lashe wa’adi na biyu a zaɓen 2027.
Ya yi wannan jawabi ne domin mayar da martani ga sabuwar haɗakar ’yan adawa da Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, da wasu shugabanni suka kafa.
NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Wasu Teloli Cika Alƙawari Majalisar wakilai ta amince da dokar ta-ɓaci a RibasA yayin taron manema labarai da Atiku ya gudanar a Abuja a ranar Alhamis, ya soki yadda Tinubu ke tafiyar da mulki, musamman batun ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas.
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da Tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, da wasu ’yan siyasa sun hallara, inda suka bayyana shirin haɗa kai domin karɓe mulki daga hannun Tinubu a 2027.
Sai dai Ganduje ya yi watsi da wannan yunƙuri, inda ya bayyana cewa tafiyar ba za ta yi tasiri ba.
“Babu wata yarjejeniya ko haɗa kai da za ta hana ’yan Najeriya sake zaɓen Tinubu a 2027,” in ji shi a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan wayar da kan jama’a, Cif Oliver Okpala, ya fitar.
Ya ce irin nasarorin da Tinubu ya samu tun bayan hawansa mulki ne zai tabbatar da nasararsa.
“Tabbas Tinubu zai sake lashe zaɓe saboda irin ci gaban da ya kawo tun bayan da ya zama shugaban ƙasa,” in ji Ganduje.
Haka kuma, ya ce wannan sabuwar haɗakar ’yan adawa ba za ta yi tasiri ba, domin ’yan siyasar da ke ciki na da manufofi daban-daban.
“Ku manta da waɗannan tarukan na ‘yan siyasa da maganganunsu marasa tushe, domin yawancinsu ba su da wata makoma ta siyasa,” in ji shi.
“Haɗin gwiwarsu – kama daga kan jam’iyyar LP zuwa PDP da SDP – na ƙunshe da mutanen da ke da ra’ayoyi daban-daban da kuma son zuciya. Ba za su taɓa iya cimma muradi na siyasa ba.”
Wannan martani na Ganduje na nuni da cewa zaɓen 2027 zai kasance mai ɗaukar hankali tare da fafatawa mai zafi tsakanin ɓangarorin siyasa.