Cocin Katolika Ya Yi Bikin Ma’aurata 21 A Neja
Published: 17th, February 2025 GMT
Bishop na Cocin Katolika da ke Kontagora, Babban Rabaran Bulus Yohanna ya gudanar da bikin aure ga ma’aurata ashirin da daya a jihar Neja.
A lokacin da yake jawabi yayin bikin daurin aurea cocin St. Mark Catholic da ke Nsanji Nkoso a karamar hukumar Magama ta jihar Neja, Bishop din ya bayyana cewa, bai kamata masoya na zama tare ba har sai coci ya tabbatar da su a matsayin ma’aurata bayan an biya sadaki da kuma bin ka’idoji.
A cewar Most Reverend Bulus Yohanna “mafi yawansu sun fi dogaro da auren gargajiya wanda a baya ya basu damar zama tare. “Kuma muna bukatar mu tabbata cewa babu wani daga cikinsu da aka tilastawa”.
“Dole ne mu ƙarfafa su su yi abin da ya dace musamman a matsayinmu na ’yan Katolika. Da wannan albarkar aure, wadannan ma’aurata ashirin da daya sun yi aure a bisa doka kuma a hukumance”.
Bishop Yohanna wanda kuma shi ne Shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen Jihar Neja, ya kara da cewa, aure alkawari ne na rayuwa wanda ya kamata a gina shi bisa soyayya
A nasa jawabin Rev. Fr. Francis Yasak Joshua, ya bayyana cewa ma’auratan su 21 sun kammala ibadar aurensu na gargajiya musamman biyan kyaututtuka ga amare, ya ce an yi musu nasihar aure na tsawon watanni uku.
Su dai wadannan ma’aurata sun kasance tare na tsawon lokaci ba tare da coci ya tabbatar da auren nasu ba, inda wadanda suka fi dadewa tare su ne wadanda suka kwashe shekaru 24 a matsayin ma’aurata, yayin da masu mafi karancin shekaru kuma su ne wadanda suka shekara daya.
Daya daga cikin wadanda suka dauki nauyin ma’auratan Lydia Ishaya ta bayyana jin dadinta inda ta ce “na yi matukar farin ciki, ina kuma rokon Allah Ya albarkaci aurensu”.
Wasu daga cikin ma’auratan sun bayyana jin dadinsu bisa yadda cocin ya tabbatar da aurensu a hukumunce.
Wasu daga cikin ma’auratan, Mista da Misis Cyprian Uche da suka kwashe shekaru 22 suna rayuwa tare, sun ce yanzu haka suna da ‘ya’ya 5, inda wasunsu sun kammala manyan makarantun gaba da sakandire, sauran kuma suna makarantar sakandare.
Daga Aliyu Lawal
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: wadanda suka
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
Sojojin kasar Yemen sun kakkabo jirgin yakin Amurka wanda ake sarrafashi daga nesa samfurin MQ-9 na 19 a jiya Lahadi da yamma a sararin samaniyar kasar.
Tashar talabijan ta Presstv daga nan Tehran ya bayyana cewa sojojin kasar ta Yemen sashen UAV wato masu kula da abinda ake kira ‘Drones’ sun bada sanarwan kakkabo jirgin yaki na Amurka ne a lokacinda yake tattara bayanai a wasu yankuna a sararin samaniyar kasar.
Masana sun bayyana cewa farashin ko wane jirgi yakin samfurin MQ-9 ya kai dalar Amurka miliyon $33, don haka ya zuwa yanzu kasar Amurka ta yi asarar dalar Amurka miliyon $600. Kafin haka dai sojojin Yemen bangaren makamai masu linzami sun bada sanarwan cilla makamai masu linzami samfurin Balistic guda biyu kan HKI, wanda ya kai ga rufe tashar jiragen sama na Bengerion a birnin Yafa (telaviv.) . Bugediya Yahyah Saree kakakin sojojin kasar ta Yemen ya bayyana cewa godiya ta tabbata ga All..saboda dukkan makaman sun cimma manufofin cillasu, wadanda suka hada da rufe tashar jiragen sama na Bengrion da tilastawa miliyoyin yahudawan sahyoniyya gudu zuwa wuraren buya.
Saree ya kammala da cewa, ayyukan soje a kan HKI da kuma Amurka zasu ci gaba har zuwa dakatar da yaki a Gaza.