Aminiya:
2025-02-20@09:15:10 GMT

NAJERIYA A YAU: Dalilan Saukar Farashin Kayan Masarufi A Kaswanni

Published: 17th, February 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Bayanai daga sassa daban-daban na Najeriya suna nuni da cewa farashin kyayyakin masarufi na ta faɗuwar a kasuwanni.

Kafin hakan dai farashin ya yi ta tashi, har ya kai ga duk abin da mutum ya saya a yau, idan ya koma kasuwa bayan kwana biyu zai ji an ce ya tashi.

NAJERIYA A YAU: Kalubalen Da Ke Durƙusar Da Gidajen Rediyo A Arewa DAGA LARABA: Dalilan Da Al’adar Zanen Fuska Ke Neman Gushewa A Kasar Hausa

Ko wadanne dalilai ne suka sa farashin kayayyakin masarufi suke ta sauka a yanzu? Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi duba ne a kan wannan batu.

Domin sauke shirin, latsa nan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farashin Kayan Abinci farashin kayan masarufi kasuwanni kayan hatsi

এছাড়াও পড়ুন:

Hajji 2025: Kamfanin Saudiyya zai maka Najeriya a Kotun Duniya

Kula da walwalar maniyyatan Najeriya ya shiga tangal-tangal bayan wani kamfanin kula da alhazai na kasar Saudiyya ya yi barazanar maka Najeriya a Kotun Hukunta Manyan Laifuka na Duniya (ICC), kan saba yarjejeniyar kwangilar aikin Hajji.

Kamfanin Mashariq Al Dhahabiah Al Mutawazi na kasar Saudiyya, wanda Hukumar Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) da Hukumomin Jin Dadin Alhazai na Jihohin suka ba wa kwangilar kula da alhazan Najeriya a aikin Hajjin 2025, ne ya yi barazanar, yana mai zargin Najeriya da yaudarar sa.

Mashariq Al Dhahabiah Al-Mutawazi ya yi barazanar maka Najeriya a Kotun Duniya ne bisa zargin Hukumar NAHCON da karya yarjejeniyar da suka kulla kan aikin kula a alhazan, musamman a Mina da Filin Arfa.

A wata wasika da ya aike wa Shugaban Ofishin Aikin Hajjin Najeriya da ke birnin Makkah a kasar Saudiyya a ranar Litinin 17 ga watan nan na Fabrairu, 2025, kamfanin ya zargi NAHCON da saba yarjejeniyar da suka kulla cewa kanfaninsu ne kadai hukumar za ta wa kwangilar aikin a bana, musammana a Mina da Arafah.

NAJERIYA A YAU: Ci-gaban Da Hukumomin Raya Shiyyoyi Za Su Samar Dattijon Neja Delta Edwin Clark ya rasu

Daga nan sai ya ba wa hukumar kwana 20 ya koma kan sharudan yarjejeniyar da suka rattaba hannu a kai, idan ba haka ba ta maka hukumar a Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC).

Binciken wakilinmu ya gano a ranar 17 ga watan Janairu ne kamfanin da NAHCON suka rattaba hannu kan yarjejeniyar kula da alhazan Najeriya a Kasa Mai Tsarki.

Amam daga bisani Kungiyar Hukumomin Jin Dadin Alhazan Jihoi suka daga kara cewa Shugaban Hukumar NAHCON, Farfesa Abdullahi Usman Saleh, ya yi gaban kansa wajen soke yarjejeniyar, kwanaki kadan kafin cikar wa’adin biyan kudi ga kamfanonin da kasashe suka ba wa aikin.

Farfesa Abdullahi Usman Saleh dai ya musanta yin gaban kansa wajen soke yarjejeniyar, yana mai cewa hukumomin Saudiyya ne suka yi.

Ana zargin NAHCON ta raba aikin gida biyu tsakanin Mashariq Al Dhahabiah Al Mutawazi da kuma kamfanin Ikram Diyafa kafin cikar wa’adin ranar 14 ga watan Janairu da hukumomin Saudiyya suka sanya.

Mashariq Al Dhahabiah Al Mutawazi na zargin NAHCON da ba shi aikin kula da alhazai 26,287, duk kuwa da cewa hukumar ta sanar cewa ta samu tantunan alhazai 52,544 da za su gudanar da aikin Hajjin, wanda hakan ke nufin hukumar ta ba wa daya kamfanin aikin kula da ragowar alhazai 26,257 ke nan.

Kamfanin ya bukaci zama na gaggawa da mahukuntan NAHCON kan lamarin domin yanke shawara kan mataki na gaba da za a dauka.

Wakilinmu ya yi iya kokarinsa domin samun martanin hukumar NAHCON a game da wannan dambarwa, amma abin ya faskara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano
  • Hana Biza: Najeriya ta cancanci a girmama ta – Babban Hafsan Tsaro
  • DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alhinin Rasuwar Edwin Clark
  • Da Muguwar Rawa, Gwamma Kin Tashi
  • Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata
  • Hauhawar farashi ya koma kashi 24 a Nijeriya — NBS
  • Hajji 2025: Kamfanin Saudiyya zai maka Najeriya a Kotun Duniya
  • NAJERIYA A YAU: Ci-gaban Da Hukumomin Raya Shiyyoyi Za Su Samar
  • FG Ta Jaddada Bukatar Samarda Sabbin Ka’idojin Visa Domin Taimakawa Kasuwancin A Duniya