HausaTv:
2025-02-20@09:11:34 GMT

Iran Ta Kira Yi Kasashen Musulmi Da Su Nuna Cikakken Goyon Bayansu Ga Falasdinu

Published: 17th, February 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci ya yi kira ga kasasnen larabawa da na musulmi da su nuna cikakken goyon bayansu al’ummar Falasdinu domin dakile makircin hadin gwiwa a tsakanin Amurka da Isra’ila na korar Falasdinawa daga gidansu.

Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar musulunci ta Iran, Abbas Arakci ya bayyana hakan ne a lokacin da ya gana da babban sakataren kungiyar kasashen larabawan yankin tekun pasha a birnin Muscat na kasar Oman a jiya Lahadi.

Babban jami’in diplomasiyyar na Iran ya kara da cewa; ya zama wajibi  a ji sauti daya daga kasashen musulmi na nuna cikakken goyon baya ga al’ummar Falasdinu.

Arakci wanda ya yi ishara da ganawa ta farko da aka yi a matakin ministocin kasashen kungiyar larabawa ta yankin tekun Pasha da kuma na Iran, Arakci ya jaddada muhimmanci cigaba da tattaunawa domin samar da fahimtar juna a tsakanin bangarorin biyu.

Ministan na harkokin wajen Iran din ya yaba wa kasashen laraabwa,musamman na yankin tekun Pasha dangane da matsayin da su ka dauka na kin amincewa da shirin Amurka da ‘yan sahayoniya na korar Falasdinawa da karfi daga Gaza. Haka nan kuma ya yi tir da furuci na tsokana da ya fito daga bakin Benjamine Netanyahu akan cewa Saudiyya ta bai wa Falasdinawa yankin da za su kafa kasarsu a cikinta.

Arakci dai ya je Oman ne domin halartar taron kungiyar kasashen da suke iyaka da tekun Indiya da shi ne karo na 8. Taken taron dai shi ne Bunkasa sabbin hanyoyi aiki tare a doron ruwa a tsakanin kasashen.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira

Kungiyoyin Falasdina mabanbanta sun yi kira da a gudanar da taron musamman na al’ummar Falasdinu domin a tattauna hanyoyin da za a dakile batun tilastawa mutanen Gaza yin hijira.

Kungiyoyin na falasdinawa sun bayyana hakan ne dai a wani taro da su ka yi a Gaza domin karfafa gwiwar mutanen wannan zirin su ci gaba da jajurcewa da tsayin dakar da suke yi, tare da kara da cewa; Babu yadda za a yi al’ummar Falasdinu su fita daga kasarsu.

Mahalarta taron na Gaza sun bayyana furucin da shugaban kasar Amurka ya yi akan  fitar da Falasdinawa daga Gaza da cewa yana nuni akan yadda Amurka da ‘yan sahayoniya su ka yi tarayya a laifukan da aka tafka akan Falasdinawa, haka nan ita kanta wannan maganar tana nufin shelanta wani sabon yakin akan al’ummar Falasdinu da hakan yake da bukatar fitar da wani matsayin na kasashen larabawa da kuma kungiyoyin kasa da kasa.

A karshe sun bukaci ganin cewa taron kasashen larabawa da za a yi nan gaba kadan, ya fito da wani tsari na ci gaban al’umma, saboda kawo karshe duk wani batu na yin hijira. Haka nan kuma sun bukaci ganin masu alaka da ‘yan mamaya daga cikin larabawa sun yanke ta.

Jami’in da yake kula da tuntubar juna a tsakanin kungiyoyi mabanbanta Khalid al-Badhash ya bayyana cewa; Duk da baranazar da hakkokin falasdinawa suke fuskanta, da kuma makirece-makircen Amurka, sai dai kuma batun kare hakkokin Falasdinawa ya sake dawowa da karfi a duniya, kuma duniyar ta gane hakikanin ‘yan mamaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Palasdinawa Ne Zasu Fayyanace Makomarsu Ba Wasu Dan Mulkin Mallaka Ba: Qalibof
  • Turkiya Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Sulhu Tsakanin Habasha Da Somaliya
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  •  Jagora: Siyasar Kasar  Iran  Ta Ginu Ne Akan Kyautata Alaka Da Kasashen Makwabta
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Da Sarkin Kasar Qatar Kan Muhimmancin Hadin Gwiwa Da Taimakekkeniya Tsakaninsu
  • Kasashen Rasha Da Amurka Sun Kuduri Anniyar Kawo Karshen Yaki A Ukraine
  • An Nuna Nezha 2 A Zama Na Musamman A Hedikwatar MDD Dake Birnin New York
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Irin Gagarumar Rawar Da Iran Ta Taka A Fegen Tsaro Yakin Tekun Pasha
  • Sarkin Qatar Zai Zayarci Tehran A Gobe Laraba
  • Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne