Rahotanni da suke fitowa daga Bukavu sun ambaci cewa ‘yan tawayen kungiyoyin M 23 da kuma AFC sun kwace iko da filin sauran jiragen sama na Kavumu wanda yake da tazarar kilo mita 45 daga birnin.

mutanen sun kauracewa zirga-zirga akan titunan birninna  Bukavu saboda rashin tabbacin abinda zai biyo baya.

Mafi yawancin ‘yan siyasa a birnin sun buya,saboda karatowar ‘yan tawayen cikin birnin.

 Wasu rahotannin suna nuni da cewa, ‘yan tawayen sun shiga cikin birnin na  Bkavu, a jiya Lahadi.

Bukavu dai shi ne birni na biyu da ‘yan tawayen su ka kama daga farkon watan Janairu zuwa yanzu, bayan da su ka shiga cikin birnin Goma.

 An Shiga Rudani A Birnin Bukavu .

Sojojin DRC da kawayensu na kasar Burundi sun janye daga cikin barikokin birnin tun a ranar Juma’a da ita ce ranar da ‘yan tawayen su ka kwace iko da filin saukar jiragen sama.

An rika jin karar bindiga da ake harbe-harbe a cikin birnin da kuma wawason da ake yi a dakunan ajiya na hukumar abinci ta duniya ( WFP).

Kustawar da kungiyoyin ‘yan tawayen suke yi a cikin biranen DRC, yana haddasa fargaba akan yiyuwar barkewar yaki a cikin yakin. Kungiyar M 23 dai tana samun goyon bayan ne daga kasar Rwanda yayin da ita gwamnatin kasar DRC take da nata kawayen a cikin yankin da su ka hada da Brundi. MDD dai ta sha yin kira da a tsagaita wutar yaki da kawo karshe fadace-fadacen da ake yi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne

A ranar 15 ga watan Fabrairu, ministocin harkokin waje na kasashen Amurka, Japan, da Koriya ta Kudu sun yi shawarwari a Munich na kasar Jamus. A cikin sanarwar hadin gwiwar da suka fitar, a karon farko, sun bayyana goyon bayansu ga yadda Taiwan za ta shiga cikin kungiyoyin kasa da kasa da suka dace, tare da jaddada muhimmancin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun Taiwan. Dangane da wannan batu, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Guo Jiakun, ya sake nanata cewa, Taiwan wani bangare ne na kasar Sin da ba za a iya raba shi da ita ba, kuma batun Taiwan lamari ne na cikin gidan kasar Sin kawai, kuma ba ta yarda da wata tsangwama daga waje ba. Shigar Taiwan cikin ayyukan kungiyoyin kasa da kasa dole ya kasance bisa ka’idar Sin daya tak a duniya. A ko da yaushe kasar Sin tana adawa da yadda wasu kasashe ke hada kai wajen kafa kananan kungiyoyi, da tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasar Sin, tare da suka da bata wa kasar Sin suna, da tayar da husuma da adawa, kana ta mika wa kasashen da abin ya shafa gamsasshen korafi.

Bugu da kari, a matsayin martani ga kwaskwarimar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta yi kan takardar sahihancin bayanai kan dangantakar Amurka da Taiwan, Guo Jia Kun ya bukaci bangaren Amurka da ya gaggauta gyara kuskuren, da kuma mutunta ka’idar Sin daya tak da sanarwoyi guda uku na Sin da Amurka, kuma ta bi a hankali wajen tinkarar batun Taiwan. (Mohammed Yahaya)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Kwalejin Koyon Tukin Jiragen Sama
  • Sojojin Sudan Sun Killace Fadar Shugaban Kasa Da Take A Hannun ‘Yan Tawayen A Birnin Khartum
  •  Rasha Ta Kakkabo Jiragen  Sama Marasa Matuki 9 Na Kasar Ukiraniya
  • Kissoshin Rayuwa. Sirar Imam Alhassan (a) 19
  • Gwamnatin Niger Ta Hana Yan Najeriya Dauke Da Passpor Ta Na ECOWAS Shiga Kasar
  • An Nuna Nezha 2 A Zama Na Musamman A Hedikwatar MDD Dake Birnin New York
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Janye Tallafin Amurka Ya Jefa Masu Fama Da Cutar HIV A Kasar Afirka Ta Kudu Cikin Fargaba
  • Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne
  • Masu Alaka