Rahotanni da suke fitowa daga Bukavu sun ambaci cewa ‘yan tawayen kungiyoyin M 23 da kuma AFC sun kwace iko da filin sauran jiragen sama na Kavumu wanda yake da tazarar kilo mita 45 daga birnin.

mutanen sun kauracewa zirga-zirga akan titunan birninna  Bukavu saboda rashin tabbacin abinda zai biyo baya.

Mafi yawancin ‘yan siyasa a birnin sun buya,saboda karatowar ‘yan tawayen cikin birnin.

 Wasu rahotannin suna nuni da cewa, ‘yan tawayen sun shiga cikin birnin na  Bkavu, a jiya Lahadi.

Bukavu dai shi ne birni na biyu da ‘yan tawayen su ka kama daga farkon watan Janairu zuwa yanzu, bayan da su ka shiga cikin birnin Goma.

 An Shiga Rudani A Birnin Bukavu .

Sojojin DRC da kawayensu na kasar Burundi sun janye daga cikin barikokin birnin tun a ranar Juma’a da ita ce ranar da ‘yan tawayen su ka kwace iko da filin saukar jiragen sama.

An rika jin karar bindiga da ake harbe-harbe a cikin birnin da kuma wawason da ake yi a dakunan ajiya na hukumar abinci ta duniya ( WFP).

Kustawar da kungiyoyin ‘yan tawayen suke yi a cikin biranen DRC, yana haddasa fargaba akan yiyuwar barkewar yaki a cikin yakin. Kungiyar M 23 dai tana samun goyon bayan ne daga kasar Rwanda yayin da ita gwamnatin kasar DRC take da nata kawayen a cikin yankin da su ka hada da Brundi. MDD dai ta sha yin kira da a tsagaita wutar yaki da kawo karshe fadace-fadacen da ake yi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Haren Kan Wasu Wurare A Gabaci Da Kuma Kudancin Kasar Lebanon

Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare a gabaci da kuma kudancin kasar Lebanon wanda yak eta yarjeniyar zaman lafiyan da HKI ta cimma da kungiyar Hizbullah mai lamba 1701 ta shekara ta 2006.

Tashar talabijin ta Presstv anan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran gwamnatin kasar Lebanon na cewa, jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan bayan kauyen taraya a gundumar ba’alabak, cikin lardin Ba’alabak Hermel, da kuma kan garin Shaara kusa da garin Jenta a dai dai kasar tsaunuka da ke yankin.

A kudancin kasar Lebanon kuma jiragen yakin HKI sun jefa makamai masu linzami har guda 4 a kan yakunan Jibaa da Snaya

Kafafen yada labaran HKI sun tabbatar da wannan labarin sun kuma nakalto sojojin kasar suna cewa sun kai hare-haren ne kan damdamalin cilla makamai masu linzami na kungiyar Hizbullah.

Sanarwan sojojin yahudawan ya ce: Sojojin HKI sun kai hari kan wuraren kungiyar Hizbullah, wadanda suke karkashin kasa a lardin Biqaa a kasar Lebanon.

Gwamnatin HKI a dole ta amince da tsagaita budewa juna wuta da kungiyar Hizbullah a ranar 27 ga watan Nuwamban shekarar da ta gabata, bayan asarorin na rayukan sojoji da tankunan yaki da kuma gine-gine masu muhimmanci wadanda kungiyar Hizbullah ta lalata a cikin yakin watanni 14 da suka fafata. Ta amince da kuduri kwamitin tsaro mai lamba 1701 na kwamitin tsaro ba tare da ta cimma ko guda daga cikin manufofin fara yakin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Hukumar Birnin Istambul Ta Dakatar Da Akram Imamoglu Daga Matsayinsa Na Magajin Garin Birnin
  • Amurka ta sake kai hare-hare Yemen
  • Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar
  • Wike Ya Kwace Filaye 4,794 A Abuja Saboda Rashin Biyan Kudin Ka’ida
  • Saree: Filin jirgin saman Ben Gurion ba shi da aminci har sai an kawo karshen yakin Isra’ila a Gaza
  • Sojojin Sudan Sun Kwace Iko Da Fadar Shugaban Kasa A Birnin Khartum
  • Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Haren Kan Wasu Wurare A Gabaci Da Kuma Kudancin Kasar Lebanon