HausaTv:
2025-02-20@08:57:02 GMT

HKI Tana Cigaba Da Hana Shigar Da Kayan Agaji Zuwa Yankin Gaza

Published: 17th, February 2025 GMT

Kwanaki 30 bayan tsagaita wutar yaki a Gaza, sojojin mamayar HKI suna cigaba da kai hare-hare a yankuna mabanbanta.

Bugu da kari, sojojin na HKI suna cigaba da rushe gidajen Falasdinawa a cikin yankin yammacin kogin Jordan.

Minsitan kudi na HKI Byetrael Smotrach ya ce, a kowace shekara za su rushe gidaje a yammacin kogin Jordan fiye da wadanda Falasdinawa suke ginawa.

Wannan dai shi ne lokacin farko da HKI ta dawo da siyasar rusau a yammacin kogin Jordan tun a 1967.

Wannan matakin na HKI yana zuwa ne a daidai lokacin da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Robio yake ziyara a Tel Aviv, kuma a lokacin da Amurkan ta bai wa HKI bama-baman MK-84 har guda 1,800.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin HKI Sun Ce Ba Zasu Fita Daga Wurare 5 A Kudancin Kasar Lebanon Ba

Sojojin HKI Sun Bada sanarwan cewa ba zasu bar wasu tuddai guda 5 a kudancin kasar Lebanon ba, har zuwa wani lokacin da basu sani ba, saboda tsaron haramtacciyar kasar.

Tashar talabijin ta Almayadin ta  kasar Lebanon, ta nakalto cewa tankunan yakin HKI sun kutsa cikin garin kafarshuba na kudancin kasar Lebanon kuma sun kafa sansanin sojojin a garin.

A jiya litinin ce yakamata sojojin HKI su fice daga kudancin kasar Lebanon da suka mamaye, amma a jiyan din ne suka bada sanarwan cewa ba zasu fita daga wurare 5 daga kudancin kasar ta Lebanon ba.   

Kafin haka bayan kwanaki 60 da tsagaita budewa juna wuta ne, yakamata sojojin HKI su fice daga kudancin kasar ta Lebanon, amma tare da shiga tsakani na gwamnatin kasar Amurka, gwamnatin kasar Lebanon ta tsawaita wanzuwar sojojin yahudawan har zuwa yau Talata 18 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025. A yau ne yakamata sojojin kasar Lebanon su karbi dukkan wuraren da sojojin yahudawan suke mamaye da su a kudancin kasar.

Har yanzun dai ba’a ji ta bakin gwamnatin kasar Lebanon dangane da wannan al-amarin.

Mai magana da yawan sojojin HKI sojojinsa ba zasu fita daga wadannan wurare 5 ba sabaoda tsaron HKI kuma a duk lokacinda suka ga mutanensu a yankin arewacin HKI zasu sami amince da zaman lafiya suna iya ficewa daga wadannan wurare.

Kafin haka dai babban sakatarin kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Qasim ya bayyana cewa sojojin HKI basu da wani uzuri na ci gaba da kasancewa a kudancin kasar Lebanon daga yau Talata 18 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Ce Tana Iya Sakin Dukkan Fursinonin Yahudawa Gaba Daya A Lokaci Guda
  • Dubban Falasdinawa Sun Kauracewa Gidajensu A Dai-Dai Lokacinta Sojojin HKI Suke Fafatawa Da Dakarun Falasdinawa
  • Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano
  • Sojojin Sudan Sun Killace Fadar Shugaban Kasa Da Take A Hannun ‘Yan Tawayen A Birnin Khartum
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Mususlunci A Iran IRGC Sun Bada Sanarwan Kai Hari A Kan HKI Karo Na Uku
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Sojojin HKI Sun Fara Ficewa Daga Wasu Wurare A Kudancin Kasar Lebanon
  • Sojojin HKI Sun Ce Ba Zasu Fita Daga Wurare 5 A Kudancin Kasar Lebanon Ba
  • Jagora : Kokarin Makiya Na Haifar Da Sabani Ya Ci Tura
  • Kotu Ta Hana Gwamnatin Tarayya Riƙe Wa Kano Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomi