Leadership News Hausa:
2025-03-23@02:06:11 GMT

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (7)

Published: 17th, February 2025 GMT

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (7)

Jami’in ilimi kwararre wanda yake aiki a bangaren ilimi shi ne kuma ke da alhakin wajen tafiyar da lamurran ilimi da suka shafi tsare- tsare da manufofin ilimi, suna tafiya kamar yadda ya dace. Ɗaya daga cikin manufofinsa da ke da amfani ita ce yin aiki kafada- kafada da Iyaye da kuma sauarn mabobin al’umma da kuma tabbatar ana tafiya tare wajen lamarin daya shafi ilimin ‘ya’yansu.

Irin hakan ya kamata ya hada masu da shirya tarurruka, tarurrukan horarwa, domin a samar da labaran da suke da alaka da ba Iyaye shawara,kai har ma da hadin kai kungiyoyin al’umma, da hukumomi,domin samar da wata da wasu hanyoyin da za su taimakawa dalibai.

Babban burin jami’in ilimi shi ne ya samu damar taimakawa domin samun sakamako mai inganci ga dalibai, iyalai, da kuma al’umma, sai kuma samar da lamarin dai rika taimakawa kowane lokaci ba tare da gajiya ba ko samun watra matsala sai dai ci gaba mai dorewa a kowane hali ga kowa da kowa.

Irin gudunmawar da jami’in ilimi ke badawa wajen samun ingancin abinda zai amfani ganewar abubuwan da ake koyawa daibai da Malamai

Jami’in ilimi yana bada muhimmiyar gudunmawa wajen tsara rayuwar karatu ta ilimin su dalibai wajen ganin ko wane lokaci ana samun ci gaba mai gamsarwa dangane da hazaƙarsu.

Hakkin su ne su tabbatar da makarantu da Malamai suna dai dai da juna su da Malamai manufa anan Malamai suyna koya abinba ya kamata kamar yadda yake cikin manhajar karatu domin samar da ilimi mai nagarta.

Ta yadda za su rika bibiyar yadda ake koyarwa su kasance babu wata amaja, hanyoyi/ dabarun koyarwa, sai yadda dalibai suke fahimtar abinda/ abubuwan da ake koya masu, domin su gano irin wuraren da su Malaman ya dace su kara maida himma domin su dalibai hazakarsu ta karu domin amfanar kansu da kuma al’umma a gaba.

Kai har ma suna wayar da kan al’umma kan muhimman lamurra kamar yadda irin halayyar da su daliban suke da ita, wadda idan aka barai abin ya ci gaba da tafiya a gaba akwai babbar matsalar da a tunkara, saboda irin hakan yana iya shafar lamarin karatun su daliban, abin kuma na iya shafar hazakarsu.

Daga karshe jami’an ilimi wasu muhimman mutane, jami’ai ne da bai kamata ayi masu rikon sakainar ka shi ba, domin suna da babban muhimmanci ga dalibai, Iyaye, da kuma Malamai gaba daya.

Irin gudunmawa da lamarin fasaha yake ga ayyukan jami’in ilimi

Lamarin bangaren fasaha yana bada muhimmiyar gudunmawar tafiyar da aikin sa saboda ta kan ba shi dama ta yin bincike, ya kuma duba da kuma/Nazari kan abinda ya samu domin ya samar da dabaraun koyarwa.Bugu da kari kuma hakan na ba shi dama yadda zai byi mu;amala da mutane kamar su Malamai, shugabannin fannin mulki, da kuma sauarn,

Malamai ko da iya kasance yana amafani ne da fashar sadarwa ta zamani wajen irin hanyoyin da zai bi ko dabaru wajen koyarwa, ya ce fasaha tana taimaka ma say a kasance koda wane lokaci ya ma yana cikin shirin abinda ka iya tasowa, fasaha k9o lamarin ta yana matukar taimakawa, domin samun hanyar da zai amfani da ita wajen gane irin tafarkin ilimin da zai yi amfani da shi domin tabbatar cewa daga karshe ‘yan makaranta ko dalibai za su samun .

Yadda jami’in ilimi yake mu’amala da sauran kwararru a bangaren ilimi

Jami’in ilimi shi en mutumin da ya kamata ya tabbatar da cewa duk wasu manufofi ko tsare- tsaren ilimi yana bi da amfani da su kamar yadda ya dace, duk kuma matakin da ake bukatar ilimi ya zama ya kasance.

Ta hanyar hada kai da wasu kwararru ta bangaren ilimi jami’in ilimi ana bukatar yin hakan domin shi jami’in ilimi ya san yadda zai tafiyar da aikinsa kamar yadda ake tsammanin hakan daga gare sa.Wannan ya hada da yi aiki da Malaman makaranta, shugabannin makaranta, mambobin tafiyar ko gudanar da makarantun,da sauran jami’an ilimi domoin a samar da kuma gudanar da sabbin tsare- tsare ko manufofin ilimi da hanya mafi dacewa da za a tafiyar ko gudanar da su.Dole ne jami’in ilimi ya rika yin lamurransa babu rufa- rufa tare da masu fada aji ya zama lalle ana ci gaba da aiwatar yin abubuwa domin amfanin kowa, wato duk masu ruwa da zaki da suka hada da dalibai da Malamai,da kuma al’umma gaba daya.

Daga karshe shi jami’in ilimi ana sa ran za iyi amfani da duk dabarun da suka kamata domin tabbatar da ana samun nasara yadda dalibai zai kai ga cimma burin mizanin da ake son ya cimmawa da kuma ci gaban lamauran ilimi baki daya.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ayyuka jami in ilimi ya kamar yadda

এছাড়াও পড়ুন:

Saura Kiris a Samin Tashin Gobarar Tankar Mai a Sakkwato

An dakile fashewar wata babbar tankar mai a Sokoto bayan da jami’an tsaro da jami’an kwana-kwana da masu bayar da agajin gaggawa suka yi gaggawar kai dauki bayan da tankar ta kife a hanyar Gagi-Nakasari a karamar hukumar Sokoto ta Kudu.

 

Wani shaidan gani da ido, Magaji Shanono ya shaidawa gidan rediyon Najeriya cewa tankar mai dauke da lita dubu arba’in da biyar na man fetur, ta wuntsila ne a lokacin da take kokarin shiga shatatalen Nakasari, inda ta zubar da mai.

 

Duk da cewa har zuwa lokacin hada wannan rahoto ba a fitar da wata sanarwa a hukumance ba, sakataren gwamnatin jihar Sokoto Muhammad Bello Sifawa ya halarci wurin da lamarin ya faru, domin ganin abin da ya faru.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Sokoto ya kuma sa ido kan matakan tsaro yayin da jami’an kashe gobara suka yi ta kokarin shawo kan lamarin.

 

Tawagar hadakar hukumar kashe gobara ta tarayya da ta jaha sun isa wurin da gaggawa, inda suka zuba kumfa don kawar da tururin wuta da hana tashin gobara a wajen.

 

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa NEMA da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar SEMA su ma sun wajen don shawo kan cunkoson jama’a, da kuma dakile hadurruka.

 

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa jami’an agajin gaggawa sun yi nasarar kwashe man zuwa wata tankar mai, inda suka kawar da illar zubewa ko fashewa.

 

Jami’an tsaro sun takaita zirga-zirga a wurin da lamarin ya faru, tare da hana mazauna wurin yunkurin diban mai.

 

NASIR MALALI

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i
  • Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira
  • Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa ta mutu
  • ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Kaduna Ta Raba Abinci, Tufafi Ga Marayu, Mabukata Da Malamai
  • Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Saura Kiris a Samin Tashin Gobarar Tankar Mai a Sakkwato
  • Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe