Malaman addini sun yi wa ’yan siyasa juyin mulki —Sule Lamiɗo
Published: 17th, February 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa Sule Lamiɗo, ya zargi malaman addini da neman ƙwace lamurran siyasar Najeriya daga hannun ’yan siyasa.
Sule Lamiɗo ya nuna damuwa bisa yadda malaman addini ke ƙara shiga harkokin siyasa, inda ya ce, a halin yanzu malaman suna yin tasiri sosai a yanayin tafiyar siyasa da kuma jefa ƙuri’a.
Ya bayyana haka ne a yayin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga fitaccen malamin Musulunci, Sheikh Yusuf Sambo Rigachikum, bisa rasuwar babban ɗansa a Jihar Kaduna.
A cikin bidiyon ta’aziyyar, an ji Sule Lamiɗo, yana cewa, malaman addini sun yi wa ’yan siyasa ƙwace, inda suke fitowa fili suna yi wa ’yan takara yaƙin neman zaɓe, tare da kiran mabiyansu su zaɓi wanda su suke goyon baya.
Tsohon Ministan Harkokin Wajen na Najeriya ya ce, “duk da ni’imar da Allah Ya yi musu na kasancewa malaman addini, amma yanzu sun koma yin kokawa da ’yan siyasa.
“Kamata ya yi malaman addini su zama iyaye masu shiryatar da al’umma, amma tunda mulki suke so, to mun ’yan siyasa za mu bar musu, mu koma gefe.”
Cikin shaguɓe ya ci gaba da cewa, “muna jira su fito su gaya mana wanda suke so mu zaɓa gwargwadon abin da suke so.” Sannan ya ce, “Idan har ana so a samu adalci da daidaito a Najeriya, to dole sai kowa ya tsaya a matsayinsa a cikin al’umma.”
Jigon Jam’iyyar adawa ta PDP, ya bayyana cewa an wayi gari rikicin cikin gida da rarrabuwar kai sun dabaibaye ƙungiyoyin da ɗarikun addini, kamar yadda jam’iyyun siyasa ke fama da waɗannan matsaloli.
Daga nan sai ya ce muddin ba a samu haɗin kai ba, tsarin siyasar Najeriya ba zai taɓa rabuwa da rikici ba.
Tasirin malamai a siyasar NajeriyaA baya malaman addini sun yi tasiri matuƙa wajen sanya magoya bayansu su yi rajistar zaɓe.
Amma a zaɓen 2023, wanda ake wa kallon rarrabuwar kai ta dabaibaye fiye da kowanne, malaman sun zarce hakan, inda suka riƙa bayyana ’yan takarar da suke goyon bayan.
Lamarin ya kai ga wasu malaman suna fitowa a huɗubobinsu, suna bayyana ɗan takarar da suke goyon baya a cikin ’yan takara.
Wasu malaman Musulunci sun rika shawarar mabiyansu da su kaɗa kuri’a bisa la’akari da addinin ’yan takara. A ɗaya ɓangaren kuma, malaman Kirista sun riƙa iƙirarin samun ilhama gane da ɗan takarar da zai lashe zaɓen na 2023. Sai dai kuma mafi yawan waɗannan iƙirarin ba su abbata da.
Dambarwar malaman addiniKo a baya-bayan nan, taƙaddama ta ɓarke tsakanin malaman Musulunci kan taron Mahaddata Al-Ƙur’ani da aka shirya gudanarwa a Abuja ranar 22 ga watan nan na Fabrairu, 2025, inda ake sa ran tara Mahaddata da Masu Zayyana da makaranta Al-Kur’ani mutum 30,000.
An ɗage taron zuwa abin da hali ya yi damuwar da wasu malaman Musulunci suka nuna kan halascin taron da kuma zargin cewa yana da alaƙa da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Takarar Muslim-MuslimIdan ba a manta ba dambarwar zaɓen Musulmi da Musulmi a lokacin takarar Shugaba Bola da mataimakinsa Kashim Shettima ya tayar da ƙura a fagen siyasar Najeriya a kakar zaɓen 2023.
Amma dai ’yan takarar sun kai labari a zaɓen saboda gagarumar goyon bayan da wasu malamai suka ba shi, suka kuma kwaɗaita wa mabiyansu alherin da ke tattare da hakan.
Bambancin addini da kabilanci sun kuma yi tasiri a yankin Kudu maso Yamma a kakar zaɓen.
A yankin Arewa muƙarraban Tinubu sun nema kuma sun samu goyon bayan manyan malaman addini wajen tallata shi. Da alama kuma irin haka ta sake kunno Kai, duba da yadda manyan ’yan siyasa suka fara shirye-shiryen zaben 2027.
Sai dai kuma akwai alama tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar LP, Mista Peter Obi, ya far sauya taku, inda a wannan karon yake ƙara matsa ƙaimi domin samun gagarumar goyon baya a yankin Arewa, inda Musulmi suka fi rinjaye.
Ana ganin halartarsa tarukan buɗa-baki a lokacin azumin watan Ramadan da kuma shigarsa harkokin da suka shafa al’ummar da kuma bayar da gudunmawar kuɗaɗe a matsayin wani salo na zawarcin al’ummar yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Siyasa Takara siyasar Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Ƙarin ’yan Najeriya za su fuskanci talauci nan da 2027 — Bankin Duniya
Bankin Duniya ya yi hasashen cewa talauci a Najeriya zai ƙaru da kashi 3.6 cikin ɗari a cikin shekaru biyar masu zuwa, ciki har da shekarar zaɓe ta 2027.
Wannan hasashe yana ƙunshe ne a cikin rahoton Bankin wanda aka fitar a lokacin taron bazara na Bankin Duniya da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) da ake yi a birnin Washington, D.C., a ƙasar Amurka.
Rahoton ya jaddada cewa duk da wasu nasarorin da aka samu a harkokin tattalin arziki a kwanakin baya, musamman a ɓangaren da ba na man fetur ba a cikin rubu’i na ƙarshe na shekarar 2024, matsalolin da suka shafi dogaro da albarkatun ƙasa da kuma raunin ƙasa na iya kawo cikas ga ci gaba.
A cewar Bankin Duniya, Najeriya, tare da wasu ƙasashe masu arzikin albarkatu da masu rauni a yankin kudu da Sahara, za su fuskanci ƙaruwar talauci —saɓanin ƙasashen marasa arzikin albarkatu, waɗanda ake tsammanin za su samu raguwar talauci cikin sauri.
’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin maganiRahoton ya bayyana cewa, “Ana hasashen talauci zai ƙaru da kashi 3.6 cikin ɗari tsakanin 2022 zuwa 2027a ƙasashe masu arzikin albarkatu da masu rauni—ciki har da manyan masu tattalin arziƙo kamar Najeriya da Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango.”
A halin da ake ciki, Sanatan da ke wakiltar Ondo ta Kudu, Jimoh Ibrahim, ya yi kira ga ƙasashen a Afirka, Bankin Duniya, da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) da su ba da fifiko ga amfani da bayanai don ci gaban Afirka.
Da yake magana a yayin taron bazara na IMF/Bankin Duniya a Washington, D.C., Amurka, Sanata Jimoh Ibrahim ya jaddada muhimmancin bayanai a ci gaban tattalin arziki da siyasa.
Ya ce, “Idan babu bayanai ba, babu wanda zai iya rage aikata laifuka yadda ya kamata ko kuma gudanar da gwamnatin da ke da nufin cimma nasarar rage talauci.”
Ya ƙara da cewa, “Bayanai kan yawan jama’a da cikakkun bayanai na mutane sun nuna cewa ya kamata ’yan ƙasa su mallaki fasfo na tantancewa domin tattara muhimman bayanai game da su wane ne su da kuma abin da suke yi.”
Sanatan ya yi gargadi ga IMF game da yin hasashe ba tare da ingantattun bayanai ba, yana mai cewa irin waɗannan hanyoyin ba su da inganci.