Aminiya:
2025-03-22@13:42:10 GMT

Malaman addini sun yi wa ’yan siyasa juyin mulki —Sule Lamiɗo

Published: 17th, February 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa Sule Lamiɗo, ya zargi malaman addini da neman ƙwace lamurran siyasar Najeriya daga hannun ’yan siyasa.

Sule Lamiɗo ya nuna damuwa bisa yadda malaman addini ke ƙara shiga harkokin siyasa, inda ya ce, a halin yanzu malaman suna yin tasiri sosai a yanayin tafiyar siyasa da kuma jefa ƙuri’a.

Ya bayyana haka ne a yayin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga fitaccen malamin Musulunci, Sheikh Yusuf Sambo Rigachikum, bisa rasuwar babban ɗansa a Jihar Kaduna.

A cikin bidiyon ta’aziyyar, an ji Sule Lamiɗo, yana cewa, malaman addini sun yi wa ’yan siyasa ƙwace, inda suke fitowa fili suna yi wa ’yan takara yaƙin neman zaɓe, tare da kiran mabiyansu su zaɓi wanda su suke goyon baya.

Tsohon Ministan Harkokin Wajen na Najeriya ya ce, “duk da ni’imar da Allah Ya yi musu na kasancewa malaman addini, amma yanzu sun koma yin kokawa da ’yan siyasa.

“Kamata ya yi malaman addini su zama iyaye masu shiryatar da al’umma, amma tunda mulki suke so, to mun ’yan siyasa za mu bar musu, mu koma gefe.”

Cikin shaguɓe ya ci gaba da cewa, “muna jira su fito su gaya mana wanda suke so mu zaɓa gwargwadon abin da suke so.” Sannan ya ce, “Idan har ana so a samu adalci da daidaito a Najeriya, to dole sai kowa ya tsaya a matsayinsa a cikin al’umma.”

Jigon Jam’iyyar adawa ta PDP, ya bayyana cewa an wayi gari rikicin cikin gida da rarrabuwar kai sun dabaibaye ƙungiyoyin da ɗarikun addini, kamar yadda jam’iyyun siyasa ke fama da waɗannan matsaloli.

Daga nan sai ya ce muddin ba a samu haɗin kai ba, tsarin siyasar Najeriya ba zai taɓa rabuwa da rikici ba.

Tasirin malamai a siyasar Najeriya

A baya malaman addini sun yi tasiri matuƙa wajen sanya magoya bayansu su yi rajistar zaɓe.

Amma a zaɓen 2023, wanda ake wa kallon rarrabuwar kai ta dabaibaye fiye da kowanne, malaman sun zarce hakan, inda suka riƙa bayyana ’yan takarar da suke goyon bayan.

Lamarin ya kai ga wasu malaman suna fitowa a huɗubobinsu, suna  bayyana ɗan takarar da suke goyon baya a cikin ’yan takara.

Wasu malaman Musulunci sun rika shawarar mabiyansu da su kaɗa kuri’a bisa la’akari da addinin ’yan takara. A ɗaya ɓangaren kuma, malaman Kirista sun riƙa iƙirarin samun ilhama gane da ɗan takarar da zai lashe zaɓen na 2023. Sai dai kuma mafi yawan waɗannan iƙirarin ba su abbata da.

Dambarwar malaman addini

Ko a baya-bayan nan, taƙaddama ta ɓarke tsakanin malaman Musulunci kan taron Mahaddata Al-Ƙur’ani da aka shirya gudanarwa a Abuja ranar 22 ga watan nan na Fabrairu, 2025, inda ake sa ran tara Mahaddata da Masu Zayyana da makaranta Al-Kur’ani mutum 30,000.

An ɗage taron zuwa abin da hali ya yi damuwar da wasu malaman Musulunci suka nuna kan halascin taron da kuma zargin cewa yana da alaƙa da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Takarar Muslim-Muslim

Idan ba a manta ba dambarwar zaɓen Musulmi da Musulmi a lokacin takarar Shugaba Bola da mataimakinsa Kashim Shettima  ya tayar da ƙura a fagen siyasar Najeriya a kakar zaɓen 2023.

Amma dai ’yan takarar sun kai labari a zaɓen saboda gagarumar goyon bayan da wasu malamai suka ba shi, suka kuma kwaɗaita wa mabiyansu alherin da ke tattare da hakan.

Bambancin addini da kabilanci sun kuma yi tasiri a yankin Kudu maso Yamma a kakar zaɓen.

A yankin Arewa muƙarraban Tinubu sun nema kuma sun samu goyon bayan manyan malaman addini wajen tallata shi. Da alama kuma irin haka ta sake kunno Kai, duba da yadda manyan ’yan siyasa suka fara shirye-shiryen zaben 2027.

Sai dai kuma akwai alama tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar LP, Mista Peter Obi, ya far sauya taku, inda a wannan karon yake ƙara matsa ƙaimi domin samun gagarumar goyon baya a yankin Arewa, inda Musulmi suka fi rinjaye.

Ana ganin halartarsa tarukan buɗa-baki a lokacin azumin watan Ramadan da kuma shigarsa harkokin da suka shafa al’ummar da kuma bayar da gudunmawar kuɗaɗe a matsayin wani salo na zawarcin al’ummar yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Siyasa Takara siyasar Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Wasu Teloli Cika Alƙawari

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A yau, mutane da dama sun fahimci muhimmancin koyan sana’a wajen dogaro da kai, maimakon dogaro da aikin gwamnati ko na kamfani.

Sai dai ana zargin wasu masu masu sana’ar hannu, musamman teloli, da rashin cika alƙawari.

NAJERIYA A YAU: Yadda Mai Karamin Karfi Zai Mallaki Muhalli Da Kudi Kalilan NAJERIYA A YAU: Guraben Ayyukan Da Aka Kasa Cikewa A Najeriya

A mafi yawan lokuta, ana samun matsala da su, musamman a lokutan bukukuwa, inda suke kasa kammala ɗinkin kayan da aka ba su ko suka yi alƙawari.

Shirin Najeriya A Yau, zai yi nazari kan dalilan da suka sa teloli ke kasa cika alƙawari da yadda hakan ke shafar kwastomomi.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufa’i Ya Yi Kadan Ya Sa Mu Bar Jam’iyyar PDP – Sule Lamido
  •  HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
  • Jagora: Amurka Ta Kwana Da Sanin Cewa Ba  Wata Riba Da Za Ta Ci Ta Hanyar Yi Wa  Iran Barazana
  • Tinubu ya ba ni riƙon Ribas don wanzar da zaman lafiya — Ibas
  • Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje
  • Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas
  • ’Yan adawa sun shirya ƙalubalantar Tinubu a zaɓen 2027 – Atiku
  • Kungiyar M-23 Ta Kasar Kongo Ta Kara Nusawa Gaba A Don Mamaye Karin Yankuna A Gabacin Kongo
  • Mutane Fiye Da 30 Ne Suka Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Dawkar Gas Ta Yi Bindiga A Abuja Na Tarayyar Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Wasu Teloli Cika Alƙawari