Ku tona asirin ’yan tsubbu —Sarkin Ilori ga malaman addini
Published: 17th, February 2025 GMT
Mai Martaba Sarkin Ilori, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, ya buƙaci a riƙa tona asirin malaman tsubbu a duk inda suke.
Sarkin wanda shi ne shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kwara, ya buƙaci malaman Musulunci da su riƙa fallasa duk masu fakewa da rigar malumta suna ayyukan tsubbu.
Basaraken ya buƙaci malaman addini da “su tsaftace harkar tasu, tare da tona asirin ɓata-garin cikinsu ga jami’an tsaro kafin miyagun su kai ga aikata munanan ayyukansu ko halaka jama’a.
Ya yi wannan kira ne bayan kisan gillar da wani mai iƙirarin malumta mai suna Abdurrahman Bello, ya yi wa wata ɗaliba ’yar ajin ƙarshe a Kwalejin Ilimi ta Jihar Kwara da ake Ilori, mai suna Hafsah Lawal.
A cikin sanarwar da basaraken ya fitar ta hannun kakakinsa, Malam Abdulazeez Arowona, a ranar Lahadi, ta umarci “malaman addini musamman limaman masallatan da ke Masarautar Ilori da ma faɗin Jihar Kwara, da su karkatar da huɗubobinsu kan inganta tarbiyya da kuma muhimmancin kare ran ɗan Adam, ba tare da la’akari da addini ko ƙabilanci ba.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan tsubbu Sarkin Ilori Sulu Gambari
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati
Sabon Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas, Vice Admiral Ibok-ete Ibas (mai ritaya), ya isa jihar domin ci gaba da aiki.
Ibas ya isa filin jirgin saman Fatakwal da misalin ƙarfe 11:25 na safiyar ranar Alhamis inda ya samu tarba daga manyan jami’ai da jami’an tsaro.
’Yan Boko Haram 7 sun miƙa wuya ga sojojin MNJTF a Borno Majalisar wakilai ta amince da dokar ta-ɓaci a RibasSabon Gwamnan, tare da rakiyar Kwamishinan ’yan sandan jihar, Olugbenga Adepoju da mataimakin babban sufeton ’yan sanda na shiyya ta 16, nan take suka wuce gidan gwamnati da ke Fatakwal.
Tuni dai Ibas ya isa gidan gwamnati inda wasu jami’an gwamnati suka zagaya da shi harabar gidan.
A yanzu haka yana ganawar sirri da manyan jami’an tsaro da wakilan gwamnatin tarayya da kuma jami’an gwamnatin jihar.
A ranar Talatar nan ne dai shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya naɗa Ɓice Admiral Ibok-Ete Ekwe Ibas a matsayin kantoman jihar Riɓers bayan da ya sanar da ƙaƙaba wa jihar dokar ta-baci. Kuma ya rantsar da shi a ranar Laraba.