Leadership News Hausa:
2025-03-23@04:05:22 GMT

Yadda Ake Fuf-Fuf

Published: 17th, February 2025 GMT

Yadda Ake Fuf-Fuf

Da farko za ku zuba Fulawa a wata roba haka sannan ku kawo Baikin Fauda ko Yis duk dai wanda za ku yi amfani da shi ku zuba, sai ku zuba madara sannan sai Gishiri kadan haka sai Qwai shima ku fasa a ciki, amma kada ya yi ruwa ko kauri kwabin.

Sannan sai ku cuccura shi kamar Bol.

Sai ku dora Mai a wuta ya yi zafi, sannan ku fara soyawa.

Bayan kin gama suya shi sai ki barbada masa sikari.

 

Yadda Ake Hada Fankek da Zuma:

Abubuwan da za ku tanada:

Fulawa, Bakin Fauda, Qwai, Madarar Ruwa, Gishiri, Bota:

 

Yadda za ku hada:

Za ku samu roba tankade fulawar a ciki duk abin da za ku yi da fulawa a bukata a tankade ta, sannan ku zuba Baikin Fauda da gishiri da madara, sai ku kwaba amma ana bukatar kwabin ya dan yi ruwa-ruwa, ana amfani da madara a matsayin ruwa.

Sannan sai ku dora Mai a wuta ko Bota duk wanda za ku yi amfani da shi, idan ya yi zafi sai ku dinga zuba kwababbiyar Fulawa kuna soyawa, amma ban da juyawa kamar dai yadda ake Sinasir.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia

A ranar Juma’a aka rantsar da sabuwar shugabar ƙasar Namibia, Netumbo Nandi-Ndaitwah domin jagorantar ƙasar wadda aka ruwaito na fuskantar ƙalubale na rashin aikin yi da talauci.

Kasancewar Netumbo Nandi-Ndaitwah mace ta biyu da aka taɓa zaɓa a matsayin shugabar ƙasa a nahiyar Afirka, kuma ta farko a Namibia na iya fuskantar ƙalubale.

Bam ya kashe mutum 4 da jikkata wasu a Borno Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira

“Idan komai ya tafi daidai, wannan zai zama kyakkyawan misali,” kamar yadda Netumbo Nandi Ndaitwah ta shaida wa shirin Podcast na BBC Africa. “Amma idan wani abu ya faru, kamar yadda zai iya faruwa ga kowace gwamnati ko da a ƙarƙashin namiji ne, akwai waɗanda za su ce: ‘saboda ni mace ce!'”

Sabuwar shugabar, mai shekara 72 a duniya ta lashe zaɓen qasar ne a watan Nuwamba inda ta lashe kashi 58% na ƙuri’un da aka kaɗa.

Nandi-Ndaitwah ta kasance daɗaɗɗiyar ƴar jam’iyyar South West Africa People’s Organisation (Swapo) – wadda take kan mulki tun lokacin da ƙasar ta samu ƴancin kai a shekarar 1990, bayan kwashe tsawon lokaci tana fafutukar ƙwatar kanta daga Afirka ta Kudu mai fama da mulkin wariya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  • Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari
  • Kasar Sin Ta Bayar Da Rijiyoyin Burtsasai 66 Ga Al’ummomin Zimbabwe Dake Fama Da Karancin Ruwa
  • Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i
  • An Bukaci Gwamnati A Kowani Mataki Da Ta Taimakawa Yaki Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban Miyetti Allah A Filato
  • Wa Ke Dandana Kudar Matakin Harajin Kwastan Da Gwamnatin Amurka Ta Dauka
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu