Leadership News Hausa:
2025-03-26@02:53:12 GMT

Gwamnan Kano Ya Gargaɗi Malamai Kan Sa Yara Aikin Wahala

Published: 17th, February 2025 GMT

Gwamnan Kano Ya Gargaɗi Malamai Kan Sa Yara Aikin Wahala

Gwamnan Kano Ya Gargaɗi Malamai Kan Sa Yara Aikin Wahala.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas

Wasu daga cikin gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP sun maka Shugaba Bola Tinubu a Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas, Similanayi Fubara.

Gwamnonin sun garzaya kotun ne domin neman fatawa game da abin da sashe na 305 na kundin mulkin ƙasar ke nufi.

Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha Juventus za ta sallami kocinta Thiago Motta

Gwamnonin da ke kan gaba a shigar da ƙarar sun haɗa da na jihohin Adamawa, Bauchi, Bayelsa, Enugu, Osun, Filato, Zamfara.

Daga cikin abubuwan da suke nema akwai neman kotun ta ɗauki matsaya kan ko sashen na 305 na kudin mulkin Nijeriya na 1999 ya bai wa shugaban ƙasa dama ya dakatar da zaɓaɓɓen gwamna da mataimakiyarsa da majalisar dokoki ta jiha, kuma ya naɗa wani gwamnan riƙo a ƙarƙashin dokar ta-ɓaci.

A ƙunshin takardun da suka gabatar wa kotun, gwamnonin sun ce dakatar da zaɓaɓɓun shugabanni da Shugaba Tinubu ya yi na cin karo da sassa na 1(2) da na 5(2) da kuma na 305 da ke ƙunshe a Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya.

Matakin na zuwa bayan huɗu cikin shida na gwamnonin yankin kudu maso kudu sun yi tir da dokar da Tinubu ya ayyana a Ribas.

Gwamnan Bayelsa Duoye Diri, wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin yankin, ya ce, “rikicin siyasar na Ribas bai kai abin da za a ayyana dokar ta-ɓaci a kai ba kamar yadda sashe na 305(3) ya tanada.”

Sai dai kuma, gwamnonin Edo da na Kuros Riba sun goyi bayan matakin na Shugaba Tinubu.

A gefe guda kuma, ƙungiyar neman shugabanci na gari ta Socio-Economic Rights and Accountability Project (Serap) ta ce ta shigar da Tinubu ƙara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja game da dakatar da gwamnan Ribas da mataimakiyarsa da majalisar dokoki “wanda ya saɓa wa doka”.

Ana iya tuna cewa, a ranar 18 ga wannan wata na Maris ne Tinubu ya dakatar da Gwamna Similanayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu da duk ’yan majalisar dokokin Jihar Ribas na tsawon watanni shida tare da ɗora tsohon Babban Hafsan Sojin Ruwa, Rear Admiral Ibok-Ete Ibas a matsayin kamtoman jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas
  • NDLEA Ta Kama Ƴar Indiya Ɗauke Da Hodar Iblis A Kano
  • UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa
  • An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano
  • Mahaifiyar Gwamnan Katsina ta rasu
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa