Leadership News Hausa:
2025-03-23@20:12:19 GMT

Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A Yau

Published: 17th, February 2025 GMT

Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A Yau

Gwamnatin Amurka ta fara aiwatar da matakan korar ‘yan Nijeriya daga ƙasar, inda ake sa ran mutane 85 za su iso Lagos, yayin da wasu 116 ke tsare.

Jakadan Amurka a Nijeriya, Richard Mills, ya bayyana haka yayin wata ziyarar ban girma da ya kai wa Ministan harkokin wajen Nijeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu, a Tafawa Balewa House da ke Abuja.

Ya bayyana cewa waɗanda ke tsare a gidan yari a Amurka ne za su kasance cikin rukuni na farko na waɗanda za a dawo da su.

Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya Amurka Da Isra’ila Sun Sake Barazanar ‘Lugudan Wuta’ A Gaza

A nata ɓangaren, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu ta bayyana damuwa kan yadda ake gudanar da tsare-tsaren korar mutanen, inda ta buƙaci da a bi ƙa’idojin da suka dace na ƙasa da ƙasa. Ta jaddada cewa dole ne a samar da hanyoyin da za su rage raɗaɗin korar, musamman ga waɗanda ba su aikata wani laifi na tashin hankali ba.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Nasiru Ahali Shahararren masanin masana’antu a Kano ya rasu

Allah Ya yi wa Alhaji Nasiru Ahali, Shugaban Kamfanin Mainasara & Sons, rasuwa.

Marigayin wanda yake shahararren masanin masana’antu ne ya rasu yana da shekara 108.

Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina Kotun ƙoli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren PDP

A cewar majiyoyin na kusa da iyalan marigayin ɗan kasuwar ya rasu ne a wani asibiti da ke Kano a daren ranar Alhamis.

Ana girmama Ahali a matsayin ɗaya daga cikin jiga-jigan masanin asalin masana’antu a Kano. Ya yi ƙoƙari ya kafa tsarin kasuwanci na yau da kullun.

A tattaunawarsa da Daily Trust a shekarar 2018, marigayi Ahli ya bayyana cewa sana’arsa ta haɗa da buga littattafai, bugu takardu, masana’antar bulo, sana’ar fasa dutse, shigo da kaya, kwangilar gama-gari, bunƙasa kadarorin rukunin gidaje, ayyukan ƙarafa da sauransu.

A saƙon ta’aziyyar da ya aike wa iyalan marigayin ta hannun Babban Daraktan Yaɗa Labarai na Gidan Gwamnatin Kano, Malam Sanusi Bature Dawakin Tofa, Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ba ga iyalansa kaɗai ba, har da jiha da ƙasa da sauran al’ummar Musulmi baki ɗaya.

Ya bayyana marigayin a matsayin ɗaya daga cikin waɗanda suka kafa masana’antu, inda ya ce shi ne ya tsara tattalin arzikin jihar tare da taka muhimmiyar rawa a tsakanin ƙananan masana’antu da manyan masana’antu a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano
  • Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  • An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar
  • Ba Gwamna Bala Ne Ya Soke Hawan Daushe Ba – Masarautar Bauchi Ta Bayyana Gaskiya
  • Trump Ya Bayyana Dalilin Rufe Gidan Rediyon Muryar Amurka
  • An Zabi ‘Yan Kasar Zimbabwe  Kuma Mace Ta Farko A Matsayin Shugabar Shugabar Kwamitin  Wasannin Olympic
  • Nasiru Ahali Shahararren masanin masana’antu a Kano ya rasu
  • Tunisiya : Kaïs Saïed, ya kori firaministansa Kamel Madouri
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka