Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A Yau
Published: 17th, February 2025 GMT
Gwamnatin Amurka ta fara aiwatar da matakan korar ‘yan Nijeriya daga ƙasar, inda ake sa ran mutane 85 za su iso Lagos, yayin da wasu 116 ke tsare.
Jakadan Amurka a Nijeriya, Richard Mills, ya bayyana haka yayin wata ziyarar ban girma da ya kai wa Ministan harkokin wajen Nijeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu, a Tafawa Balewa House da ke Abuja.
A nata ɓangaren, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu ta bayyana damuwa kan yadda ake gudanar da tsare-tsaren korar mutanen, inda ta buƙaci da a bi ƙa’idojin da suka dace na ƙasa da ƙasa. Ta jaddada cewa dole ne a samar da hanyoyin da za su rage raɗaɗin korar, musamman ga waɗanda ba su aikata wani laifi na tashin hankali ba.
এছাড়াও পড়ুন:
Nasiru Ahali Shahararren masanin masana’antu a Kano ya rasu
Allah Ya yi wa Alhaji Nasiru Ahali, Shugaban Kamfanin Mainasara & Sons, rasuwa.
Marigayin wanda yake shahararren masanin masana’antu ne ya rasu yana da shekara 108.
Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina Kotun ƙoli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren PDPA cewar majiyoyin na kusa da iyalan marigayin ɗan kasuwar ya rasu ne a wani asibiti da ke Kano a daren ranar Alhamis.
Ana girmama Ahali a matsayin ɗaya daga cikin jiga-jigan masanin asalin masana’antu a Kano. Ya yi ƙoƙari ya kafa tsarin kasuwanci na yau da kullun.
A tattaunawarsa da Daily Trust a shekarar 2018, marigayi Ahli ya bayyana cewa sana’arsa ta haɗa da buga littattafai, bugu takardu, masana’antar bulo, sana’ar fasa dutse, shigo da kaya, kwangilar gama-gari, bunƙasa kadarorin rukunin gidaje, ayyukan ƙarafa da sauransu.
A saƙon ta’aziyyar da ya aike wa iyalan marigayin ta hannun Babban Daraktan Yaɗa Labarai na Gidan Gwamnatin Kano, Malam Sanusi Bature Dawakin Tofa, Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ba ga iyalansa kaɗai ba, har da jiha da ƙasa da sauran al’ummar Musulmi baki ɗaya.
Ya bayyana marigayin a matsayin ɗaya daga cikin waɗanda suka kafa masana’antu, inda ya ce shi ne ya tsara tattalin arzikin jihar tare da taka muhimmiyar rawa a tsakanin ƙananan masana’antu da manyan masana’antu a jihar.