Gwamna Umar Namadi  ya kaddamar da aikin gina titin Kanya Babba (Kwanar Duzau) zuwa Kankare zuwa Ballada zuwa Duzau zuwa Danhill zuwa Kyambo zuwa Mundu zuwa Goron Maje.

Aikin wanda aka bayar da shi kan kudi naira biliyan 6 da miliyan 300, wani muhimmin mataki ne a yunkurin gwamnatin jihar na inganta ababen more rayuwa da  hanyoyin sada yankuna.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Namadi ya jaddada muhimmancin hanyoyin, wajen samar da ci gaban tattalin arziki, da inganta hanyoyin samar da ababen more rayuwa, da inganta rayuwar al’ummar yankin.

Ya sake jaddada kudurin gwamnatinsa na samar da ingantattun ababen more rayuwa da za a dade ana amfana da su.

Ya kuma bayyana cewa,  ana sa ran  da zarar an kammala  aikin zai bunkasa kasuwanci, da saukaka kalubalen sufuri, da bude sabbin hanyoyin tattalin arziki ga mazauna yankin.

Malam Umar Namadi ya ce, gwamnatin jihar ta bayar da kwangilar gina sabbin hanyoyi arba’in da bakwai na tsawon sama da kilomita dari tara a jihar.

Ya bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da ayyuka a dukkan hanyoyin da aka bayar da aikinsu.

A nasa jawabin kwamishinan ayyuka da sufuri na jihar Injiniya Gambo S Malam ya ce an bayar da aikin gina hanyar kanya Babba, zuwa Duzau zuwa Goron Maje akan kudi sama da naira biliyan shida.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, Karamar Ministar Ilimi Farfesa Suwaiba Ahmed Babura ce ta kaddamar da aikin.

Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da, mataimakin gwamnan jihar Jigawa Injiniya Aminu Usman, da kakakin majalisar dokokin jihar Alhaji Haruna Aliyu Dangyatum da sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim da dai sauransu.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro ta Kano

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaron al’umma ta Jihar Kano mai suna ‘Kano State Security Neighborhood Watch.’

Gwamnan ya sanya hannu kan dokar ne tare da wasu ƙarin dokokin guda biyu, waɗanda suka haɗa da dokar gyara hukumar sufuri ta jihar da kuma wadda ta kafa cibiyar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa ta jihar.

Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓi Gubar harsashi ta jikkata mutane dama a Zamfara

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature ya fitar ta ce gwamnan ya amince da dokokin ne a zaman majalisar zartarwar jihar na 25 da ya gudana a fadar gwamnatin jihar.

Hakan na zuwa ne bayan dokar samar da rundunar tsaron ta bi matakan da suka kamata a majalisar dokokin jihar.

Kano dai na fama da matsaloli irin na rikice-rikicen dabanci da ƙwacen waya, lamarin da ya yi sanadiyar ajalin mutane da dama.

Me Abba ya ce?

A jawabinsa bayan rarraba hannu dokokin, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ganin an samu ribar dimokuraɗiyya da kuma bunƙasa tattalin arzikin jihar cikin ƙanƙanin lokaci.

Ya kuma jaddada cewa gwamnati ta tsaya tsayin daka a ƙoƙarinta na ɓullo tare da aiwatar da manufofi da tsare-tsare da nufin inganta rayuwar al’ummar Jihar Kano.

Gwamna Yusuf ya bayyana jin daɗinsa dangane da irin goyon baya da haɗin kai da jama’a ke ba su, inda ya buƙaci da su ci gaba da gudanar da ayyukansu domin cimma manufofin gwamnatin.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi
  • UNICEF Ya Bukaci Hadin Kai Don Inganta Rayuwar Kananan Yara A Jigawa
  • Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwo
  • ASUU Reshen Jami’ar KASU Ta Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa Jihar Jigawa Kayayyakin Noma Na Sama Da Naira Biliyan 5
  • Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro ta Kano
  • Hajji 2025: Kamfanin Saudiyya zai maka Najeriya a Kotun Duniya
  • Hamas Ta Sanar Da Shahadar Wani Jagoranta Da HKI Ta Kashe A Lebanon
  • Gwamnan Kano Ya Gargaɗi Malamai Kan Sa Yara Aikin Wahala