Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Tituna Akan Kudi Naira Biliyan 6.3
Published: 17th, February 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da aikin gina titin Kanya Babba (Kwanar Duzau) zuwa Kankare zuwa Ballada zuwa Duzau zuwa Danhill zuwa Kyambo zuwa Mundu zuwa Goron Maje.
Aikin wanda aka bayar da shi kan kudi naira biliyan 6 da miliyan 300, wani muhimmin mataki ne a yunkurin gwamnatin jihar na inganta ababen more rayuwa da hanyoyin sada yankuna.
Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Namadi ya jaddada muhimmancin hanyoyin, wajen samar da ci gaban tattalin arziki, da inganta hanyoyin samar da ababen more rayuwa, da inganta rayuwar al’ummar yankin.
Ya sake jaddada kudurin gwamnatinsa na samar da ingantattun ababen more rayuwa da za a dade ana amfana da su.
Ya kuma bayyana cewa, ana sa ran da zarar an kammala aikin zai bunkasa kasuwanci, da saukaka kalubalen sufuri, da bude sabbin hanyoyin tattalin arziki ga mazauna yankin.
Malam Umar Namadi ya ce, gwamnatin jihar ta bayar da kwangilar gina sabbin hanyoyi arba’in da bakwai na tsawon sama da kilomita dari tara a jihar.
Ya bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da ayyuka a dukkan hanyoyin da aka bayar da aikinsu.
A nasa jawabin kwamishinan ayyuka da sufuri na jihar Injiniya Gambo S Malam ya ce an bayar da aikin gina hanyar kanya Babba, zuwa Duzau zuwa Goron Maje akan kudi sama da naira biliyan shida.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, Karamar Ministar Ilimi Farfesa Suwaiba Ahmed Babura ce ta kaddamar da aikin.
Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da, mataimakin gwamnan jihar Jigawa Injiniya Aminu Usman, da kakakin majalisar dokokin jihar Alhaji Haruna Aliyu Dangyatum da sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim da dai sauransu.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
Gwamnatin Jihar Jigawa ta sake jaddada bukatar bin dokar da ta hana kiwon dare da makiyaya ke yi a fadin jihar domin rage hadurra a tituna, wanda ke haddasa asarar rai ko shiga mawuyacin hali a sanadiyar raƙuman da ke bi ta manyan tituna.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan yayin da ya karbi bakuncin tawagar Kungiyar Makiyayan Raƙuma ta Yammacin Afirka a ziyarar girmamawa da suka kai Fadar Gwamnati a Dutse.
Ya ce gwamnatin ta himmatu matuka wajen ganin ta kula da lafiyar al’ummar jihar.
Malam Umar Namadi ya kara da cewa, wannan gwamnati tana da masaniya kan haramtattun ayyukan wasu makiyaya, musamman waɗanda ke shigowa daga ƙasashe makwabta.
Ya bayyana shirin gwamnatin jihar na yin rajistar makiyaya domin sauƙaƙa samunsu
idan buƙatar hakan ta taso.
Namadi ya nuna damuwarsa kan yawan asarar rayuka da raunuka daban-daban da jama’a ke fuskanta sakamakon yawaitar raƙuma da ke tsallaka manyan hanyoyi kowacce rana.
A nasa jawabin, babban sakataren Kungiyar Makiyayan Yammacin Afirka a Najeriya, Abubakar Mustapha Andaza, ya ce sun kai ziyarar ne domin su gabatar da kansu ga gwamnan, tare da neman shawarwarin gwamnatin jihar kan yadda za su gudanar da harkokinsu yadda ya dace.
Usman Muhammad Zaria