Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Tituna Akan Kudi Naira Biliyan 6.3
Published: 17th, February 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da aikin gina titin Kanya Babba (Kwanar Duzau) zuwa Kankare zuwa Ballada zuwa Duzau zuwa Danhill zuwa Kyambo zuwa Mundu zuwa Goron Maje.
Aikin wanda aka bayar da shi kan kudi naira biliyan 6 da miliyan 300, wani muhimmin mataki ne a yunkurin gwamnatin jihar na inganta ababen more rayuwa da hanyoyin sada yankuna.
Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Namadi ya jaddada muhimmancin hanyoyin, wajen samar da ci gaban tattalin arziki, da inganta hanyoyin samar da ababen more rayuwa, da inganta rayuwar al’ummar yankin.
Ya sake jaddada kudurin gwamnatinsa na samar da ingantattun ababen more rayuwa da za a dade ana amfana da su.
Ya kuma bayyana cewa, ana sa ran da zarar an kammala aikin zai bunkasa kasuwanci, da saukaka kalubalen sufuri, da bude sabbin hanyoyin tattalin arziki ga mazauna yankin.
Malam Umar Namadi ya ce, gwamnatin jihar ta bayar da kwangilar gina sabbin hanyoyi arba’in da bakwai na tsawon sama da kilomita dari tara a jihar.
Ya bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da ayyuka a dukkan hanyoyin da aka bayar da aikinsu.
A nasa jawabin kwamishinan ayyuka da sufuri na jihar Injiniya Gambo S Malam ya ce an bayar da aikin gina hanyar kanya Babba, zuwa Duzau zuwa Goron Maje akan kudi sama da naira biliyan shida.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, Karamar Ministar Ilimi Farfesa Suwaiba Ahmed Babura ce ta kaddamar da aikin.
Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da, mataimakin gwamnan jihar Jigawa Injiniya Aminu Usman, da kakakin majalisar dokokin jihar Alhaji Haruna Aliyu Dangyatum da sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim da dai sauransu.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Za a mayar da tubabbun ’Yan Boko Haram cikin al’umma – Gwamna Buni
Gwamnatin Yobe ta bayyana shirinta na mayar da tubabbun mayaƙan Boko Haram cikin al’ummarsu da aka yi wa shirin kawar da tsattsauran ra’ayi, gyara da sake haɗewa da iyalansu ƙarƙashin rundunar Operation Safe Corridor (OPSC).
Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ne ya bayyana haka a ranar Alhamis a Damaturu lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar rundunar OPSC ƙarƙashin jagorancin babban hafsan tsaron Nijeriya Janar Christopher Musa.
Hisbah ta warware rigingimu 565 da lalata katan 51 na barasa a Yobe Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwajiGwamna Buni, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Alhaji Idi Gubana ya bayyana ziyarar a matsayin wata dama ta tuntuɓar juna da haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da gwamnatin jihar.
Ya koka da yadda rikicin da aka kwashe sama da shekaru 15 ana yi ya laƙume rayukan dubban mutane a Yobe, da lalata dukiyoyin jama’a da na masu zaman kansu tare da raba magidanta da dama da garuruwansu na asali.
Gwamnan ya ce gwamnatin jihar ta gane cewa, ba dukkan ’yan ƙungiyar ta’addancin ne ke shiga cikin kisan kai ba, yana mai cewa tsarin kishin ƙasa ya ba da damar ceto da kuma mayar da waɗanda suka nuna nadama ya zuwa ga al’ummominsu.
“Mun yi imanin cewa, an tura wasu mutane shiga cikin ’yan ta’adda ta hanyar ƙarfi ko koyarwar aƙida.”
“Tare da ci gaba da ƙoƙarinsu, za su iya tuba, gyarawa da komawa rayuwa ta yau da kullun a matsayin ‘yan ƙasa da ke da ‘yanci.” In ji Buni.
Gwamnan ya ce tubabbun ‘yan Boko Haram 390 da suka haɗa da ‘yan asalin Jihar Yobe 54 ne za su kammala karatu tsakanin ranakun 14 zuwa 19 ga Afrilu.
Ya ce, jihar ta samar da wasu tsare-tsare ta hanyar ma’aikatar Jinƙai da kula da bala’o’i domin tabbatar da sake dawo da su cikin al’umma yadda ya kamata.