HKI Ba Zata Yarda A Kafa Kasar Palasdinu Ba, Saboda Barazana Ce Ga Wanzuwar HKI
Published: 17th, February 2025 GMT
Ministan tsaron HKI Israel Katz ya bayyana cewa gwamnatin HKIba zata bar a kafa kasar Falasdinu ba, saboda hakan barazana ce ga samuwar HKI.
Israek Kazt ya bayyana haka ne a lokacin ganawar jami’an gwamnatin HKI da tawagar kasar Amurka.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a taron su da tawagar kasar ta Amurka a yau.
Wasu kafafen yada labarai sun nakalto wasu manya manyan jami’an sojojin kasar suna tunanin dakatar da tsagaita wuta da suka kulla da Hamas. Banda haka suna ganin shawarar shugaba kasar Amurka Donal Trump n araba gaza da Falasdinawa ne kawai zai tabbatar da wanzuwar HKI.
Kafin haka dai Banyamin Natanyahu ya fadawa kafafen yada labarai kan cewa Falasdinawa suna da damar su bar Gaza su je inda suka ga dama, idan sun bukaci hakan, amma idan bas u yi ba, to mai yuwa a kashesu gaba daya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Karin Sinawa Suna Son Kashe Kudi
A kwanakin baya, bankin Deutsche, banki mafi girma na kasar Jamus ya yi bayani game da yanayin kashe kudi ta kasar Sin cewa, karin Sinawa suna kara son kashe kudi. Bisa sabon rahoton da bankin ya gabatar, an ce, idan aka kwatanta da na shekarar bara, yawan masu kashe kudi na kasar Sin yana karuwa, kashi 52 cikin dari na wadanda suka bayyana ra’ayoyinsu a binciken sun ce suna son kara kashe kudi, adadin da ya kai matsayin koli a shekara daya da ta gabata. Kididdigar da gwamnatin kasar Sin ta gabatar ita ma ta shaida wannan yanayi, a farkon watanni biyu na shekarar bana, yawan kudin kayayyakin da aka sayar a kasar Sin ya kai Yuan triliyan 8 da biliyan 373 da miliyan 100, karuwar da ta zarce zaton da aka yi.
Me ya sa karin Sinawa suke son kashe kudi? Farfesa Wang Xiaosong na kwalejin ilmin tattalin arziki na jami’ar Renmin ta kasar Sin ya yi nuni da cewa, tun daga shekarar bara, tattalin arzikin Sin ya samu karuwa, kudin shiga na jama’ar kasar shi ma ya karu, lamarin da ya zama silan karuwar kudi da ake kashewa. Kana gwamnatin kasar Sin ta gabatar da jerin matakan tallafi don sa kaimi ga fadada kashe kudi a kasar.
Kasar Sin tana da mutane fiye da biliyan 1 da miliyan 400, tana daya daga cikin manyan kasuwanni na duniya. Kamfanin McKinsey ya yi hasashen cewa, ya zuwa shekarar 2030, mazaunan biranen kasar Sin za su sa kaimi ga karuwar kashe kudi ta duniya da kashi 91 cikin dari, biranen kasar Sin 700 za su samar da gudummawa ga karuwar kashe kudi na biranen duniya da dala triliyan 7, wanda ya kai kashi 30 cikin dari. Kashe kudi ya sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki, ana kara kashe kudi a kasar Sin, babu shakka za a samu sabon karfin raya tattalin arzikin duniya. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp