Iran: Himmati Yana Halattar Taro Dangane Da Matsalolin Da Suka Addabar Kasashe Masu Tasuwa
Published: 17th, February 2025 GMT
Ministan tattalin arziki na kasar Iran Abdunnaser Himmati yana halatan taro dangane da matsaloli da kuma dammakin da kasashen masu tasowa suka fama da su a birnin Riyad na kasar Saudiya.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa Himmati yana halattan wannan taro na kwanaki biyu ne tare da gayyatar tokwaransa na kasar Saudiya da kuma shugaban asusun lamuni ta duniya wato IMF.
Labarin ya kara da cewa gwamnatin JMI dai tana kokarin ganin ta kyautata dangantaka ko ta ina da kasashen larabawa na yankin tekun da sauran makobta.
Taron ya hada da ministan kudi na kasar Saudiya, gwamnann babban bankin kasar, da kuma wadanda suke ruwa da tsaki a harkkin kasuwanci na kasar ta saudia, sun hadu da tokwarorinsa na Iran inda suka tattauna kan al-amuran tattalin arziki a tsakaninsu.
Himmati ya bukaci karin hadin kai da kasar saudiya don zuba jari a fannoni daban-daban a kasar Iran. Har’ila yau sun tattauna batun harkokin kudade a lokacin ayyukan hajji.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Palasdinawa Ne Zasu Fayyanace Makomarsu Ba Wasu Dan Mulkin Mallaka Ba: Qalibof
Shugaban majalisar dokokin kasar Iran Muhammad Bakir Qalibof ya bayyana cewa falasdinawa masu kasa ne zasu fayyace makomar kasarsu, don haka shirin da wasu manya-manyan kasashen duniya suke dashi a kan makomar Falasdinu da Falasdinawa ba dai-dai bane kuma zamu yi yaki da shi.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Teran ta nakalto shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammada Bakir Qolibft yana fadar haka a taron shuwagabannin majalisun dokoki na kasashen Asia a birnin Baku na kasar Azaibaijan.
Qolibof ya kuma kara da cewa shirin shugaban kasar Amurka yake yi na kwace gaza da kuma inda za’a maida Falasdinawa ba zai kai ga nasara ba.
Qalibof ya yi allawadai wadai da shugaba Trump kan shishigin da yake yi a cikin al-amuran Falasdinawa, da kuma yin watsi da kokarin Falasdinawa a gaza suke yi don kwato kasarsu.
Ya ce Iran ba za ta amince da duk wata kasa mai jin tana da karfi wacce za ta dorawa falasdinawa tunaninsa ba.
Shugaban majalisar ya bayyana cewa yakin da HKI ta fafata da falasdinawa a Gaza, da kuma kungiyar Hizbulla a kasar Lebanon, sun bayyana raunin HKI a fili, wannan duk tare da dukkan tallafin da take samu daga kasashen yamma musamman Amurka.
Daga karshe ya ce dole ne a sami yentacciyar kasar Palasdinu mai zaman kanta nan gaba.