Aminiya:
2025-03-23@22:32:19 GMT

Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Yobe

Published: 17th, February 2025 GMT

’Yan sanda sun yi nasarar kama wasu mutane biyu da ake zargi da laifin yi wa wata yarinya ‘yar shekara 12 fyaɗe a kauyen Jalingo da ke Ƙaramar Hukumar Tarmuwa a Jihar Yobe.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, ya fitar a Damaturu ranar Litinin.

Gwamnati ta raba wa mata tallafin awakai na N5bn a Katsina Yadda na yi wa budurwar da muka haɗu a Facebook gunduwa-gunduwa —Matashi

Ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:30 na yammacin ranar 15 ga watan Fabrairu, inda waɗanda ake zargin suka kai yarinyar wani kango a jeji suka keta mata haddi.

Rahoton na cewar, “Hedikwatar ‘yan sandan jihar reshen Ƙaramar Hukumar Tarmuwa ta cafke waɗanda ake zargin da suka haɗa baki tare da yi wa yarinyar ‘yar shekara 12 fyade, inda suka ji mata munanan raunuka.”

“Kamar yadda majiyar ke nunawa tuni wannan yarinya ta samu kulawa cikin gaggawa, yayin da aka miƙa waɗanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na jiha (SCID) da ke Damaturu domin gudanar da bincike mai zurfi akan su,” in ji Abdulkarim.

Haka nan a wani samame da aka yi, kakakin ya ce an kuma kama wasu ɓata gari uku a unguwar Alimari da ke Damaturu bisa zargin ɗauke wani babur tare da lalata shi kwanan nan a unguwar Abbari da ke cikin birnin na Damaturu.

A cewarsa, waɗanda ake zargin sun ɓoye babur ɗin ne da wasu kayayyaki a wani gini da ba a kammala ba a yankin.

Ya ce jami’an nasu da ke aiki a ofishin ‘yan sanda na A Divisional, sun kai farmaki gidan tare da cafke waɗanda ake zargi da aikata laifin satar babur ɗin.

Har ila yau, SP Abdulkarim ya ce hedikwatar ‘yan sanda ta Gujba tare da haɗin gwiwar ‘yan banga sun ceto wani matashi daga hannun masu garkuwa da mutane a ƙauyen Daddawel.

Ya ce matashin da aka yi garkuwa da shi a ranar 12 ga watan Fabrairu, ya shakami iskar ’yanci ne bayan wani artabu tsakanin masu garkuwar da ‘yan sanda da ‘yan sa kai, lamarin da ya tilasta wa masu laifin gudu suka bar wanda aka yi garkuwar da sauran kayayyaki ciki har da wata bindiga guda ɗaya.

Abdulkarim ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya yaba da ƙoƙarin jami’an rundunar, inda ya ba da tabbacin ɗorewar yaƙi da miyagun laifuka a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: fyaɗe Jihar Yobe yarinya waɗanda ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina

Dakarun Sojin Najeriya sun kuɓutar da mutum 84 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Kankara a Jihar Katsina.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na jihar, Nasir Mu’azu, ya bayyana cewa sojojin runduna ta 17 tare da tallafin jiragen yaƙi sun kai farmaki maɓoyar ’yan ta’adda da ke yankin Sanusi Dutsin-Ma da tsaunukan Pauwa.

’Yan bindiga sun sace shugaban kasuwar kayan miya ta Akinyele a Oyo Farashin fetur na iya tashi bayan Dangote ya daina sayar da mai a Naira

Ya ce a yayin farmakin dakarun sun kashe wasu daga cikin ’yan bindiga sannan suka kuɓutar da waɗanda aka sace.

Daga cikin mutanen da aka ceto, akwai maza bakwai, mata 23, da yara 54.

Kwamishinan ya ce gwamnatin jihar ta yaba wa sojojin bisa ƙoƙarinsu, kuma tuni aka samar da abinci da kulawa ga mutanen da aka kuɓutar, kafin a mayar da su ga iyalansu.

Ya ƙara da cewa Gwamnatin Katsina ba za ta yi sulhu da ’yan ta’adda ba, domin tana da niyyar ci gaba da yaƙi da su har sai an daƙile matsalar garkuwa da mutane a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]
  • EFCC Ta Cafke Mutum 21 Bisa Zarginsu Da Zambar Intanet A Bauchi
  • Chelle Ya Fara Da Ƙafar Dama A Super Eagles 
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • Bam ya kashe mutum 4 da jikkata wasu a Borno
  • Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira
  • Gaggan Masu Garkuwa Da Mutane 10 Da Kayan Aikinsu Sun Shiga Hannu A Kano
  • Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina
  • Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum