HausaTv:
2025-03-23@23:31:22 GMT

Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon

Published: 17th, February 2025 GMT

Bangaren kungiyar Hamas da ke dauke da makamai ya tabbatar da shahadar wani daga cikin jami’in kungiyar a wani harin Isra’ila.

Muhammad Ibrahim Shaheen, ya yi shahada ne a wani harin da wani jirgin yakin Isra’ila ya kai a Sidon.

Kassam Brigades ta bayyana shi  a matsayin wanda ya yi tsayin daka kan zalincin Isra’ila, ciki har da lokacin yakin Gaza.

Ita ma Isra’ila ta tabbatar da kashe jami’in na Hamas a harin da ta ce ta kai kan a Lebanon

Sojojin Isra’ila sun yi ikirarin kai harin ta sama a Sidon, inda suka ce sun kashe wani “dan ta’adda” Bafalasdine.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta kokarin ganin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma tsakanin Isra’ila da Hamas ta daure.

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya fada jiya Lahadi cewa, tawagar tattaunawa ta kasar za ta je birnin Alkahira domin tattaunawa kan aiwatar da yarjejeniyar.

Sanarwar ta kara da cewa, da farko dai tawagar za ta fara tattaunawa ce kan ci gaba da aiwatar da mataki na daya na yarjejeniyar tsagaita wutar, kana za a ba ta umarni a kan ci gaba da tattaunawa game da kashi na biyu, bayan taron majalisar tsaron Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Haren Kan Wasu Wurare A Gabaci Da Kuma Kudancin Kasar Lebanon

Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare a gabaci da kuma kudancin kasar Lebanon wanda yak eta yarjeniyar zaman lafiyan da HKI ta cimma da kungiyar Hizbullah mai lamba 1701 ta shekara ta 2006.

Tashar talabijin ta Presstv anan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran gwamnatin kasar Lebanon na cewa, jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan bayan kauyen taraya a gundumar ba’alabak, cikin lardin Ba’alabak Hermel, da kuma kan garin Shaara kusa da garin Jenta a dai dai kasar tsaunuka da ke yankin.

A kudancin kasar Lebanon kuma jiragen yakin HKI sun jefa makamai masu linzami har guda 4 a kan yakunan Jibaa da Snaya

Kafafen yada labaran HKI sun tabbatar da wannan labarin sun kuma nakalto sojojin kasar suna cewa sun kai hare-haren ne kan damdamalin cilla makamai masu linzami na kungiyar Hizbullah.

Sanarwan sojojin yahudawan ya ce: Sojojin HKI sun kai hari kan wuraren kungiyar Hizbullah, wadanda suke karkashin kasa a lardin Biqaa a kasar Lebanon.

Gwamnatin HKI a dole ta amince da tsagaita budewa juna wuta da kungiyar Hizbullah a ranar 27 ga watan Nuwamban shekarar da ta gabata, bayan asarorin na rayukan sojoji da tankunan yaki da kuma gine-gine masu muhimmanci wadanda kungiyar Hizbullah ta lalata a cikin yakin watanni 14 da suka fafata. Ta amince da kuduri kwamitin tsaro mai lamba 1701 na kwamitin tsaro ba tare da ta cimma ko guda daga cikin manufofin fara yakin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • MDD da EU sun yi tir da wargaza yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da Isra’ila ta yi
  •  HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
  • Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Haren Kan Wasu Wurare A Gabaci Da Kuma Kudancin Kasar Lebanon
  • An kori shugaban hukumar leken asiri ta cikin gidan Isra’ila