HausaTv:
2025-04-14@18:05:38 GMT

Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon

Published: 17th, February 2025 GMT

Bangaren kungiyar Hamas da ke dauke da makamai ya tabbatar da shahadar wani daga cikin jami’in kungiyar a wani harin Isra’ila.

Muhammad Ibrahim Shaheen, ya yi shahada ne a wani harin da wani jirgin yakin Isra’ila ya kai a Sidon.

Kassam Brigades ta bayyana shi  a matsayin wanda ya yi tsayin daka kan zalincin Isra’ila, ciki har da lokacin yakin Gaza.

Ita ma Isra’ila ta tabbatar da kashe jami’in na Hamas a harin da ta ce ta kai kan a Lebanon

Sojojin Isra’ila sun yi ikirarin kai harin ta sama a Sidon, inda suka ce sun kashe wani “dan ta’adda” Bafalasdine.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta kokarin ganin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma tsakanin Isra’ila da Hamas ta daure.

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya fada jiya Lahadi cewa, tawagar tattaunawa ta kasar za ta je birnin Alkahira domin tattaunawa kan aiwatar da yarjejeniyar.

Sanarwar ta kara da cewa, da farko dai tawagar za ta fara tattaunawa ce kan ci gaba da aiwatar da mataki na daya na yarjejeniyar tsagaita wutar, kana za a ba ta umarni a kan ci gaba da tattaunawa game da kashi na biyu, bayan taron majalisar tsaron Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina

Jami’an tsaro sun samu nasarar kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ake kira Gwaska Ɗan Ƙarami da wasu mayaƙa 100 a Jihar Katsina.

Kwamishinan Harkokin Cikin Gida na Jihar Katsina, Dokta Nasir Mu’azu ya bayyana matakin a matsayin wata gagarumar nasara a yaƙi da ’yan bindiga ake yi a jihar.

An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba — Ganduje

“Abin farin ciki ne ga jihar, domin wannan nasara ta taimaka wajen wargaza ayyukan ’yan bindigar da ke addabar garuruwa da ƙauyukan da ke ƙananan hukumomin Faskari da Kankara da Bakori da Malumfashi da kuma Kafur,” in ji Kwamishinan.

Ya bayyana cewa runduna ta 17 ta sojin Nijeriya tare da ɓangaren sojin saman ƙasar ne suka ƙaddamar da hare-haren a ranar 10 ga watan Afrilun shekarar 2025 a dabar ɓarayin daji a Mununu Bakai da Zango da Jeka Arera da Malali, da kuma Ruwan Godiya duka a cikin ƙananan hukumomin Kankara da Faskari.

Haɗin gwiwar jami’an tsaron ƙasar ne suka ƙaddamar da harin a ranar Juma’a wanda ya yi sanadin kisan Gwaska — wanda ya kasance mataimakin shahararren ɗan bindiga Malan, shugaban ISWAP a yankin Arewa Maso Yamma.

“Hare-haren da suka yi daidai kan ɓarayin, bisa bayanan sirrin da aka samu, sun yi silar kashe wani wanda ake nema ruwa-a-jallo da aka fi sani da Gwaska, wanda mataimaki ne ga wani shugaban ’yan bindiga mai alaƙa da ISWAP,” in ji shi.

“Bayanan sirri sun tabbatar da cewa kwanan nan ne Gwaska ya yi ƙaura daga Ƙaramar Hukumar Danmusa zuwa dajin Munumu.

Rahotonni sun ce sojojin sun lalata maɓoyar ’yan bindigar da dama a sassan jihar a lokacin harin, tare da ƙwato da kuma lalata wasu manyan bindigogi masu jigida da waɗanda aka ƙera a cikin gida.

Harin na zuwa ne bayan da a farkon mako ’yan bindigar suka yi garkuwa da mutum 43 mazauna ƙauyukan Maigora da ke yankin Ƙaramar Hukumar Dandume.

Kazalika, dakarun tsaro sun ƙaddamar da wani aiki da sanyin safiyar ranar 10 ga watan Afrilun shekarar 2025, a hanyar da ɓarayin daji ke bi a Dutsen Wori gefen hanyar Dandume zuwa Kandamba, da ke wajen garin Dandume a kan iyaka da ƙananan hukumomin Faskari da Sabuwa.

Aikin da aka aiwatar da misalin ƙarfe 3:45 na dare ya yi silar kashe ɓarayi shida ciki har da shugabansu, yayin da sauran ɓarayin suka tsere da raunukan bindiga.

Bayanai sun nuna cewa dakarun sun ƙwace mashina bakwai yayin da saura huɗu suka tsere cikin daji.

An bi sawun ɓarayin ne daga dabarsu da ke Maigora/Doroyi cikin Ƙaramar Hukumar Faskari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • Jiragen Saman Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Luguden Wuta Kan Asibitin Baptist Da Ke Gaza
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji