A kwanan nan ne dai aka gudanar da taron kolin Kungiyar Tarayyar Afirka wato AU karo na 38, inda aka zabi ministan harkokin wajen kasar Djibouti Mahmoud Ali Youssouf a matsayin sabon shugaban hukumar gudanarwar AU na tsawon shekaru hudu. Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya taya shi murna a yau 17 ga wata, ya kuma jaddada cewa, kasar Sin a shirye take ta yi hadin gwiwa tare da Youssouf, da sabuwar hukumar gudanarwa ta AU.

Yayin da yake amsa tambayoyi a gun taron manema labaru na yau, Guo Jiakun ya bayyana cewa, kasar Sin tana kallon dangantakarta da AU daga mahanga mai muhimmanci kuma na dogon lokaci. Yana mai cewa “A halin yanzu, zaman lafiya da ci gaba a Afirka na fuskantar sabbin damammaki da kalubale, kuma kasar Sin a shirye take ta yi hadin gwiwa tare da shugaba Mahmoud Ali Youssouf da sabuwar hukumar ta AU, da ci gaba da nuna goyon baya ga kungiyar AU wajen taka muhimmiyar rawa don aiwatar da dunkulewar kasashen Afirka, da samar da murya mai karfi a harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya, tare da sa kaimi ga raya zurfafar dangantakar dake tsakanin Sin da AU, da hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka, da jagorantar hadin kan kasashe masu tasowa don inganta kai da sa kaimi ga zamanantarwa tare. (Mohammed Yahaya)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Suke Da Hakkin Yanke Shawarar Makomar Kaarsu Ba Amurka Ba

Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Iran ce zata yanke shawara a nan gaba kan matsayin kasarta, ba Trump ba

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian a yammacin jiya Alhamis ya jaddada cewa: Iran ce take da hakkin yanke shawara kan makomarta ba Trump ba, yana mai jaddada wajabcin sauya ra’ayi domin dakile duk wani takunkumin da Trump ya kakabawa kasarsa.

A jawabin da shugaba Pezeshkian ya gabatar a wajen taron shugabannin lardin Tehran ta yamma da majalisar gudanarwa ta garuruwan Mallard, Shahriar da Quds, shugaba Pezeshkian ya bayyana cewa, ma’anar gudanarwa ita ce sanin damammaki da barazana a ciki da wajen kasar da kuma sanin irin karfi da ake da shi.

Shugaban kasar ya jaddada cewa: Trump na fadin wani abu, kuma wasu mutane sun saba da abin da Trump yake so. Mene ne Trump yake son aikatawa? A nan mu ne za mu yanke shawarar yadda za mu tafiyar da makomarmu. Idan ba Iran ba ta canza ra’ayinta ba, to, ta sanya wa kanta takunkumi a hukumance, amma idan ta sauya ra’ayinta, Trump ba zai kai ma burinsa ba, kuma komai yawan takunkumin da zai Sanya kan kasar Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
  • Iran Ta Yi Tir Da Shugaban Hukumar IAEA Saboda Sanya Siyasa Da Daukan Bangare A Jawansa Na Baya Bayan Nan
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Suke Da Hakkin Yanke Shawarar Makomar Kaarsu Ba Amurka Ba
  • Jakadan Sin Dake Najeriya Ya Gana Da Karamar Ministar Harkokin Wajen Kasar
  • Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Kwalejin Koyon Tukin Jiragen Sama
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Da Sarkin Kasar Qatar Kan Muhimmancin Hadin Gwiwa Da Taimakekkeniya Tsakaninsu
  • Tinubu Ya Taya Babban Mai Tace Labarai Na LEADERSHIP, Ishiekwene Murnar Cika Shekaru 60
  • Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri