HausaTv:
2025-03-23@22:41:31 GMT

Nijar Na Son Kulla Yarjejeniya Kafofin Yada Labarai Na Iran

Published: 17th, February 2025 GMT

Nijar ta bayyan fatanta na ganin ta kulla yarjejeniya da kafofin yada labarai na Iran.

Wannan bayanin na kunshe ne a bayyannin da jakadan Nijar a Tehran Malam Seydou Ali Zataou, ya yi a ganawarsa da shugaban hukumar gidan radiyo da talabijin sashen kasashen waje na Iran, Ahmad Norozi a wannan Litinin.

Bangarorin sun bayyana kyakyawan fatan musayar bayanai da shirye shirye a tsakaninsu da nufin karya laggon kafofin yada labarai na kasashen yamma dake yada gurbatattun bayanai da rahotanni kan kasashen.

jakadan na NIjar, ya kuma yi tinu da irin kyakyawar alakar dake tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 “Yan Ta’adda Sun Kai Hari Akan Masu Salla A Jamhuriyar Nijar

Kamfanin dillancin labarun “Anatoli” na Turkiya ya ambato cewa; Ministan harkokin cikin gida na Jamhuriyar Nijar Mohamed Toumba  ne ya bayar da labarin cewa, mutane da dama sun kwanta dama sanadiyyar harin da su ka kai wa masu masu salla  a garin Fonbita dake gundumar  Kokorou.

Rahotannin sun tabbatar da cewa adadin masu sallar da su ka yi shahada sun kai 57wasu 13 kuma su ka jikkaya.

Jami’an tsaro a Jamhuriyar Nijar sun tabbatar da cewa kungiyar “Da’esh’ ta ‘yan ta’adda ta sanar da cewa ita ce ta kai wannan harin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jakadan Sin A Amurka: Mayar Da Karin Haraji Makami Kaikayi Ne Da Zai Koma Kan Mashekiya
  • Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
  •  “Yan Ta’adda Sun Kai Hari Akan Masu Salla A Jamhuriyar Nijar
  •  Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!
  • An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar
  • Kasar Sin Ta Bayar Da Rijiyoyin Burtsasai 66 Ga Al’ummomin Zimbabwe Dake Fama Da Karancin Ruwa
  • An Yi Tarukan Tattaunawar Kasa Da Kasa Kan More Damammakin Sin A Havana Da Doha
  • Hajjin Bana: Maniyata 3, 155 Suka Yi Rijista a Kano
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka