Nijar Na Son Kulla Yarjejeniya Kafofin Yada Labarai Na Iran
Published: 17th, February 2025 GMT
Nijar ta bayyan fatanta na ganin ta kulla yarjejeniya da kafofin yada labarai na Iran.
Wannan bayanin na kunshe ne a bayyannin da jakadan Nijar a Tehran Malam Seydou Ali Zataou, ya yi a ganawarsa da shugaban hukumar gidan radiyo da talabijin sashen kasashen waje na Iran, Ahmad Norozi a wannan Litinin.
Bangarorin sun bayyana kyakyawan fatan musayar bayanai da shirye shirye a tsakaninsu da nufin karya laggon kafofin yada labarai na kasashen yamma dake yada gurbatattun bayanai da rahotanni kan kasashen.
jakadan na NIjar, ya kuma yi tinu da irin kyakyawar alakar dake tsakanin kasashen biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
“Yan Ta’adda Sun Kai Hari Akan Masu Salla A Jamhuriyar Nijar
Kamfanin dillancin labarun “Anatoli” na Turkiya ya ambato cewa; Ministan harkokin cikin gida na Jamhuriyar Nijar Mohamed Toumba ne ya bayar da labarin cewa, mutane da dama sun kwanta dama sanadiyyar harin da su ka kai wa masu masu salla a garin Fonbita dake gundumar Kokorou.
Rahotannin sun tabbatar da cewa adadin masu sallar da su ka yi shahada sun kai 57wasu 13 kuma su ka jikkaya.
Jami’an tsaro a Jamhuriyar Nijar sun tabbatar da cewa kungiyar “Da’esh’ ta ‘yan ta’adda ta sanar da cewa ita ce ta kai wannan harin.