Gobara ta yi ajalin uwa da ’ya’yanta a Ondo
Published: 18th, February 2025 GMT
Ana fargabar cewa gobara ta yi ajalin wata uwa da ’ya’yanta biyu a yankin Onipakala da ke Ƙaramar Hukumar Ondo West a Jihar Ondo.
Bayanai sun ce musibar ta auku ne da tsakar daren Lahadi yayin da jama’a ke sharar barci, lamarin da ya jefa makwabta cikin zullumi.
Saudiyya ta bai wa Kano da Abuja tallafin dabino albarkacin watan Ramadana Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a YobeAminiya ta ruwaito cewa, zuwa wayewar gari Litinin, matar da ’ya’yanta —Bukola da Ifeoluwa— sun ƙone ƙurmus a sakamakon gobarar.
Wani maƙwabcinsu da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce tun tsakar dare gobarar ta tashi amma ana ji ana gani ta rutsa da mutanen uku saboda babu wata hanya da za a iya ceto rayuwarsu.
Shugaban ƙungiyar masu gidajen haya, Mista Adegbulu, ya bayyana takaicin yadda ’yan kwana-kwana suka gaza kawo ɗauki a sanadiyyar rashin ruwan kashe gobara da suka yi iƙirarin ya yanke musu.
“Mun kira su a wayar tarho a lokacin da gobarar ta tashi, amma sai suka shaida mana cewa ruwa da sauran sunadaran kashe gobarar ya yanke musu.
“Kuma nan da nan ma jami’in ya kashe wayarsa,” in ji shi.
Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin ofishin Hukumar Kashe Gobara da ke Akure, amma lamarin ya ci har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.
Mazauna da dama sun bayyana alhini kan aukuwar lamarin da kawo yanzu ba a kai ga gano musabbabinsa ba.
Funmilayo Odunlami-Omisanya, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, ta tabbatar da faruwar lamarin.
Ta bayyana cewa tuni an miƙa gawarwakin mamatan zuwa Babban Asibitin Ondo.
Wannan iftila’i na zuwa ne ƙasa da mako guda da wasu ƙananan yara biyu ’yan gida ɗaya suka riga mu gidan gaskiya a sanadiyyar wata gobara da ta tashi a wani gida a birnin Akure.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ya ya Gobara jihar Ondo Uwa
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja
Ana fargabar matafiya da dama sun rasu bayan kifewar wani kwalekwale ɗauke da ’yan kasuwa a yankin Kogin Neja.
Hatsarin kwalekwalen ya auku ne ƙauyen Sokun da ke yankin Ƙaramar Hukumar Lapai, a sakamakon iska mai ƙarfi da ta haddasa juyawar igiyar ruwan.
Shaidu sun ce hatsarin ya auku ne a yayin da kwalekwalen ke ɗauke da fasinjoji da kuma buhunan shinkafa kimanin 200 daga ƙauyen Bugge na Jihar Kogi a zuwa ƙauyen Sokun na Jihar Neja a ranar Laraba da dare.
Wani mazaunin yankin, Baba Alhassan, ya shaida wa wakilinmu cewa, ba a kai ga tantance ainihin yawan fasinjojin da ke cikin kwalwkwalen a lokacin da lamarin ya faru ba, amma an yi asarar duk buhunan shinkafar a hastarin.
NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan NajeriyaYa bayyana cewa daga cikin mamatan har da wani mai sana’ar POS da ƙaninsa ’yan asalin ƙauyen Alaba da ke Ƙaramar Hukumar Lapai
Daraktan Hukumar ba da Agajin Gaggawa na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa ana ci gaba da aikin ceto da ƙoƙarin gano ainihin musabbabin hatsarin da kuma irin asarar da ta haifar.
Mazauna yankin sun bayyana cewa, “Sufurin ruwa shi ne kaɗai hanyar da ta rage da muke amfani da ita domin kai kayanmu kasuwanni saboda hanyar ta yi mummunan lalacewa.”
Wata ’yar kasuwa a yankin mai suna Fatima Muhammad, ta bayyana cewa, saboda nisan tafiyar, fasinjoji sukan yi tafiyar dare domin su isa kasuwa washegari da safe.
Fatima ta ce, “Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne sufuri. Da kwalekwale muka dogara wajen kai kayanmu kasuwa. Wani lokaci kwalekwalen na ɗaukar lodi fiye da kima. Sai ka ga kwalekwale mai ƙarfin ɗaukar mutane 100 ya kwashi sama da haka. Amma ban ga laifin fasinjojin ba, musamman masu son su isa da wuri.”
Jama’ar yankin sun yi kira ga Gwamnatin Jihar Neja da ta Tarayya da su samar da wadatattun rigunan kariya da jiragen ruwa na zamani sannan su aiwatar da tsauraran hukunci kan masu karya doka.