Leadership News Hausa:
2025-03-24@11:26:19 GMT

Da Dama Sun Rasu Yayin Da NAF Ta Kai Wa ‘Yan Bindiga Hari A Katsina

Published: 18th, February 2025 GMT

Da Dama Sun Rasu Yayin Da NAF Ta Kai Wa ‘Yan Bindiga Hari A Katsina

Ya ce harin da aka kai ta sama ya yi sanadin kashe ‘yan ta’adda da dama tare da dakile harin da suka kai wa jami’an rundunar ‘yansanda (PMF) da jami’an tsaro na cikin unguwanni (Community Watch Corps, CWC) na jihar Katsina.

 

AVM Akinboyewa ya bayyana cewa, an kaddamar da harin ne a matsayin martani ga bayanan sirri da ke nuna cewa, an kai harin ta’addanci a wani sansanin PMF da ke cikin al’umma, inda aka ce, ‘yan bindigar sun kashe jami’an PMF biyu da CEC hudu.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Haaretz: Sojojin Isra’ila Suna Kan Shirya Kai Wa Gaza Hari Ta Kasa

Jaridar HKI ta “Haaretz” ta buga wani labara da yake cewa, sojojin HKI suna shirin kai wa Gaza gagarumin hari ta kasa bisa cikakken goyon bayan Donald Trump na Amurka.

Jaridar ta kuma ce; Harin na kasa da sojojin za su kai a cikin zirin Gaza,gagarumi ne a karkashin sabon babban hafsan hafsoshin soja Iyal Zamir.

 Har ila yau, marubucin rahoton Amos Har’el ya kuma kara da cewa; A wannan karon sun yi imani da cewa gagarumin harin da za su kai wa Gaza zai sa su cimma manufofin da su ka sanya a gaba da aka kasa a cikin tsawon shekara daya da rabi.

Daga cikin wadannan manufofin da ‘yan sahayoniyar suke son cimmawa da akwai rusa makamai da karfin kungiyar Hamas.

Jaridar ta kuma ce a daidai lokacin da ake maganar tattaunawa domin musayar fursunoni, HKI tana shirin sake amfani da karfin soja domin sake shimfida ikonta a cikin Gaza baki daya.

Danagne da rawar da Amurka take takawa a cikin abubuwan da suke faruwa, iyalan fursunoni wadanda suke da takardun zama, ‘yan Isra’ila a lokaci daya kuma Amurkawa, gwamnatin Amurka ba sanar da su cewa, Donald Trump yana cikin shirin bai wa Benjamine Netanyauhu cikakken goyon bayan idan ya zartar da fara kai hare-hare ta kasa akan Gaza. Haka nan kuma an sanar da cewa, ko kadan Trump ba zai yi wa Netanyahu matsin lamba akan dole sai ya koma kan batun musayar fursunoni ba ta ruwan sanyi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • An Kashe Askarawa 6 da ‘Yan Sa-kai 4 A Zamfara 
  • Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas
  • Mahaifiyar Gwamnan Katsina ta rasu
  •  Haaretz: Sojojin Isra’ila Suna Kan Shirya Kai Wa Gaza Hari Ta Kasa
  •  “Yan Ta’adda Sun Kai Hari Akan Masu Salla A Jamhuriyar Nijar
  • Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri
  • ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe
  • Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina