A ranar 15 ga watan Fabrairu, ministocin harkokin waje na kasashen Amurka, Japan, da Koriya ta Kudu sun yi shawarwari a Munich na kasar Jamus. A cikin sanarwar hadin gwiwar da suka fitar, a karon farko, sun bayyana goyon bayansu ga yadda Taiwan za ta shiga cikin kungiyoyin kasa da kasa da suka dace, tare da jaddada muhimmancin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun Taiwan.

Dangane da wannan batu, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Guo Jiakun, ya sake nanata cewa, Taiwan wani bangare ne na kasar Sin da ba za a iya raba shi da ita ba, kuma batun Taiwan lamari ne na cikin gidan kasar Sin kawai, kuma ba ta yarda da wata tsangwama daga waje ba. Shigar Taiwan cikin ayyukan kungiyoyin kasa da kasa dole ya kasance bisa ka’idar Sin daya tak a duniya. A ko da yaushe kasar Sin tana adawa da yadda wasu kasashe ke hada kai wajen kafa kananan kungiyoyi, da tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasar Sin, tare da suka da bata wa kasar Sin suna, da tayar da husuma da adawa, kana ta mika wa kasashen da abin ya shafa gamsasshen korafi.

Bugu da kari, a matsayin martani ga kwaskwarimar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta yi kan takardar sahihancin bayanai kan dangantakar Amurka da Taiwan, Guo Jia Kun ya bukaci bangaren Amurka da ya gaggauta gyara kuskuren, da kuma mutunta ka’idar Sin daya tak da sanarwoyi guda uku na Sin da Amurka, kuma ta bi a hankali wajen tinkarar batun Taiwan. (Mohammed Yahaya)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen

Jiragen yakin Amurka sun kai sabbin hare-hare kan wasu yankunan a kasar Yemen a safiyar a jiya Asabar, wadanda suka Baida Sa’ada da kuma Hudaidah wadanda sune sake zafafa yaki a ciki kasar na baya-bayan nan.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kafafen yada labarai na kasar ta Yemen na fadar cewa jiragen yakin kasar ta Amurka sun kai  hare-hare har 5 a kan makarantar koyon sana’o’ii na Al-sawma  da ke lardin  Al-Bayda a jiya Asabar .

Labarin ya kara da cewa makarantar ita ce babbar makaranta a yankin, kuma cibiyar ilmi mafi girma. Har’ila yau labarin ya bayyana cewa jiragen yakin kasar ta Am,urka sun kai hare-hare har guda 3 a kan garin Al-Sahleen daga cikin yankunan Kitif da kuma Al-Bogee daga cikin lardin Sa’ada.

Labarin ya kara da cewa wannan yankin yana daga cikin yankunan da ake fafatawa da sojojin  Amurka, kuma suna yawaita kan hare-hare a cikinsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Kasar Gabon Brice Oligui Nguema Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar
  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas