Aminiya:
2025-04-14@23:17:15 GMT

NAJERIYA A YAU: Ci-gaban Da Hukumomin Raya Shiyyoyi Za Su Samar

Published: 18th, February 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A kwanakin baya ne dai Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙirƙiro sababbin hukumomin raya shiyyoyin ƙasar nan da nufin kawo musu ci-gaba.

Gabanin ƙirƙirar waɗannan hukumomin, gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ce ta fara kirkirar hukumar raya yankin Neja Delta bayan wasu ƙalubale da suka dabaibaye yankin.

Na baya-bayan nan ita ce Hukumar Raya yankin Arewa ta Tsakiyar ƙasar nan bayan da ’yan yankin suka nace da yin ƙorafin cewa an mayar da su saniyar ware.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Saukar Farashin Kayan Masarufi A Kaswanni DAGA LARABA: Dalilan Da Al’adar Zanen Fuska Ke Neman Gushewa A Kasar Hausa

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan irin ci-gaban da waɗannan hukumomin raya shiyyoyi za su samar ga al’ummar ƙasa.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Makiya suna cike da takaici da fushi kan ci gaban da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take samu

A yayin ganawarsa da manyan kwamandojin sojojin kasar Iran a yau Lahadi, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa; Ci gaban da Iran ta samu ya fusata da kuma kara takaicin masu mugun nufi kan lasar ta Iran. Yana mai bayyana cewa, tabbas akwai rauni a fannonin da suka shafi tattalin arziki da ya kamata a magance.

Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya yi la’akari da cewa; Sojojin kasar suna matsayin kariya ta al’umma da kuma mafakar al’umma daga duk wani mai wuce gona da iri, sannan kuma ya jaddada wajibcin ci gaba da bunkasa shirye-shirye da kayan aiki da tsare-tsare don sauke wannan nauyi na kasa. Ya kara da cewa: Ci gaban da kasar ta samu ya fusata da kuma kara takaicin masu adawa da Iran, kuma ko shakka babu akwai raunin da ya faru a fannonin da suka shafi tattalin arziki da babu shakka akwai bukatar a magance shi. Jagoran ya bayyana shirye-shiryen kayan aikin sojojin a matsayin ma’ana inganta karfin makamansu da inganta tsarin su da kuma yadda suke rayuwa. Ya kara da cewa, “Bugu da ƙari, shirye-shiryen kayan aiki, shirye-shirye ne na gudanar da tsare-tsare – wato imani da manufa da sako da kuma tabbatar da halaccin hanyar – wadanda suke da matukar muhimmanci, kuma akwai ƙoƙari na makiya na neman murguda su.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar
  • Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Abincin karnuka ya fi namu —Fursunonin Najeriya
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
  • Najeriya Tana Fatan Samun Dalar Amurka Biliyan $200 A Ayyukan Sararin Samaniya